Da dumi-dumi: An harbe mutum 11 har lahira a sabon harin da aka kai Katsina

Da dumi-dumi: An harbe mutum 11 har lahira a sabon harin da aka kai Katsina

  • 'Yan bindiga sun kai mummunan hari kauyen Dan-Kumeji da ke karamar hukumar Kankara a jihar Katsina
  • An tattaro cewa sun kashe mutane 11 tare da jikkata wasu shida a harin da suka kai da misalin karfe 11:30 na dare
  • Zuwa yanzu ba a ji ta bakin rundunar 'yan sandan jihar ba kan lamarin

Rahotanni sun kawo cewa ‘yan bindiga sun harbe akalla mazauna kauyen Dan-Kumeji da ke karamar hukumar Kankara a jihar Katsina 11 har lahira.

Jaridar Daily Trust ta tattaro cewa mutane shida da suka samu raunuka a harin suna karbar magani a asibiti a yanzu haka.

Da dumi-dumi: An harbe mutum 11 har lahira a sabon harin da aka kai Katsina
Yan bindiga sun harbe mutum 11 har lahira a sabon harin da aka kai Katsina Hoto: Daily Trust
Asali: UGC

Wani mazaunin garin, Abdulmumini Sani, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a wata hira ta wayar tarho, ya ce maharan sun afka wa kauyen da misalin karfe 11:30 na dare inda suka fara harbi ba kakkautawa, jaridar Thisday ta kuma ruwaito.

Kara karanta wannan

Rashin tsaro: 'Yan Najeriya ba su cancanci wannan ba - Majalisar wakilai

Ya ce:

“Lokacin da mutanenmu suka gan su, sai suka fara gudu don tsira, ba tare da sanin cewa wasu daga cikin maharan sun yi kwanton bauna a wurare masu mahimmanci ba. Sai kawai suka fito suka fara harbin wadanda ke kokarin tserewa daga harin.”

Ya kara da cewa a safiyar yau Juma'a an kirga gawarwaki kusan 11 kuma ana ci gaba da shirye-shiryen binne gawarwakin da aka gano.

Kakakin ‘yan sanda a Katsina, SP Gambo Isah, bai tabbatar da faruwar lamarin ba har zuwa lokacin hada wannan rahoton.

‘Yan bindiga sun karbi N68m da sababbin babura kafin su fito da ‘Yan Islamiyyan Tegina

A wani labarin, mun ji cewa sauran ‘daliban makarantar Islamiyyar Tanko Salihu da aka dauke a garin Tegina, jihar Neja, sun fito ne bayan an kara wa ‘yan bindiga kudi.

Kara karanta wannan

Gidaje 5 na hafsoshin soja 'yan bindiga suka balle a NDA Kaduna

Jaridar Daily Trust ta samu labari cewa sai da aka kara wa ‘yan bindigan kudin fansa bayan sun ki karbar Naira miliyan 50 da aka kai masu a baya.

‘Yanuwa da iyayen wadannan yara sun yi kokarin kara hada Naira miliyan 30 bayan sun biya Naira miliyan 20 domin a ceto yaran a watan Yuni.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng