Babbar Magana: A Karon Farko, Babban Limamin Makka Sheikh Sudais Ya Naɗa Mata Mataimakansa

Babbar Magana: A Karon Farko, Babban Limamin Makka Sheikh Sudais Ya Naɗa Mata Mataimakansa

  • Shugaban hukumar kula da masallai masu tsarki na Makka da Madina, Sheikh Sudais ya naɗa mata mataimakansa
  • Wannan ne dai karon farko da mace zata rike babban mukami a hukumar kula da masallatai
  • Hakanan hukumar ta sanar da cewa zata fara baiwa mata horo don haɓɓaka ayyukan matan a masallatan biyu

Saudi Arabia - Kasar Saudiyya ta bayyana naɗa mata a manyan mukamai na hukumar dake kula da masallatai biyu mafiya daraja dake Makka da Madina.

A ranar Litinin ɗinnan ne kafar watsa labarai ta Al-Arabiyya tv, wadda mallakin Kasar Saudiyya ne, ta bada rahoto kan cigaban.

Rahoton BBC Hausa ya bayyana cewa Shugaban hukumar, Sheikh Abdulrahman Al-Sudais ya naɗa mata guda biyu a matsayin mataimakansa.

Sheikh Abdulrahman Al-Sudais
Babbar Magana: A Karon Farko, Babban Limamin Makka Sheikh Sudais Ya Naɗa Mata Mataimakansa Hoto: saudi24news.com
Asali: UGC

Matan da shugaban hukumar ya naɗa sun haɗa da Dakta Al-Anoud Al-Aboud da kuma Dakta Fatima Al-Rashoud.

Za'a baiwa mata horo mai taken 'Hayyak'

Rahoton Al-Arabiyya ya kara cewa hukumar kula da masallatan biyu zata horad da mata ma'aikata 320 yan asalin Saudiyya.

Kara karanta wannan

Da Duminsa: Tankar mai ta fadi, ta nike mutane da dama a Ibadan

Hukumar ta bayyana cewa horon mai taken 'Hayyak' zai taimaka wajen haɓɓaka ayyukan mata a masallatai biyu mafiya daraja, kamar yadda BBC ta ruwaito.

A baya ma'aikatar shari'a ta naɗa mata 100

Wannan ba shine karon farko ba, inda a shekarar da ta gabata ma'aikatar shari'a ta kasar Saudiyya ta sanar da naɗa mata 100 a ɓangarori da dama na shari'a.

Jagoran sabbin waɗanda aka naɗa a mukaman, Dr Hala al-Tuwaijri, tace:

"Gwamnatin Saudiyya ta saka taimakon mata a gaba, inda take ɗorawa a kan tsare-tsarenta na baya."

Yariman Saudiyya mai jiran gado, Muhammad Bin Salman, shine ya kirkiro da wani kudiri mai taken Muradin 2030, wanda zai baiwa mata damar fitowa a dama dasu a kowane bangaren gwamnati.

A wani labarin kuma Gwamna Zulum Ya Bayyana Yadda Yake Farin Ciki da Yan Boko Haram/ISWAP Suke Tuba a Borno

Gwamnatin jihar Borno ta bayyana jin daɗinta yayin da ake kara samun karuwar yan ta'adda suna tuba su mika makamansu ga sojoji a jihar, Kamar yadda dailytrust ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba da Shugaban Jam'iyyar APC

Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Borno, Alhaji Babakura Abba-Jato, shine ya bayyana haka jim kaɗan bayan kammala taron tsaro a Maiduguri.

Asali: Legit.ng

Online view pixel