Ku shiga siyasa idan kuna son Najeriya ta samu ci gaba, Gwamna ya bukaci Malaman addini

Ku shiga siyasa idan kuna son Najeriya ta samu ci gaba, Gwamna ya bukaci Malaman addini

  • Siyasa a kowane mataki ba na shugabanni da ‘yan siyasar da ke gwamnati bane kawai; 'yan kasa suna da rawar ganin da za su taka
  • Wannan shine ra'ayin Gwamna Seyi Makinde lokacin da yayi magana a cocin Christ Revival Miracle Church a Ibadan a ranar Lahadi, 8 ga watan Agusta
  • Gwamnan na Oyo ya ce hanya daya da 'yan kasa za su samu irin shugabancin da suke so shi ne su shiga siyasa

Ibadan, Oyo - Ga gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo, harkar siyasa ta dukkanin masu sha'awar ci gaban ƙasa da bunkasar ƙasar ne.

Wannan shine dalilin da ya sa gwamnan a ranar Lahadi, 8 ga watan Agusta, ya ƙarfafa wa malaman cocin Christ Revival Miracle Church, Ibadan, gwiwar cewa su shiga siyasa.

Ku shiga siyasa idan kuna son Najeriya ta samu ci gaba, Gwamna ya bukaci Malaman addini
Gwamna Seyi Makinde ya bukaci malaman addini da su shiga a dama da su a harkar siyasa Hoto: Seyi Makinde
Asali: Facebook

Gwamna Makinde ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya halarci wani taron cocin wanda babban jagoransa, Reverend Peter Folorunso Owa ya shirya.

Kara karanta wannan

Sarkin Musulmi ya bayyana 'yan Boko a matsayin matsalar Najeriya

A cikin jawabinsa, Makinde ya bayyana cewa ta hanyar shiga cikin ayyukan siyasa ne 'yan ƙasa za su iya samun jerin shugabannin da za su taimaka musu wajen cimma burinsu na gama gari.

Ya ce:

"Na kuma karfafa wa duk wanda ke a nan gwiwar cewa ya shiga siyasa da shugabanci, saboda ta hanyar shigar mu ne jihar mu da kasar mu za su samu irin shugabancin da suke so."

A wani labari na daban, jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta bukaci gwamna Aminu Masari na jihar Katsina da ya daina jaje kan hauhawar hare-haren 'yan bindiga a jiharsa.

A yayin karbar bakuncin Faruk Yahaya, shugaban dakarun sojin kasa wanda ya kai ziyara jihar Katsina a ranar Alhamis, Masari ya ce goma daga cikin kananan hukumomin jihar na fuskantar harin 'yan bindiga a kullum.

Kamar yadda TheCable ta ruwaito, ya ce rashin tsaron da jihar Katsina ke fuskanta na hana shi bacci.

Kara karanta wannan

Ku kai yakin har zuwa mafakar makiya, COAS, Janar Yahaya ya umarci sojoji

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng