Hotunan Wani Gwamna da Ya Rungumi Sana'ar Hada Takalmi da Takalman da Yake Haɗawa

Hotunan Wani Gwamna da Ya Rungumi Sana'ar Hada Takalmi da Takalman da Yake Haɗawa

  • Gwamnan jihar Abia, Okezie Ikpeazu, ya nuna wa yan Najeriya irin takalmin da ya iya haɗawa
  • A baya dai, gwamnan ya sanar da shiga makarantar koyon haɗa takalma domin nuna wa yan Najeriya muhimmancin hakan
  • Ya kuma yi kira ga yan Najeriya da su rinka siyan kayan da aka yi su a ƙasa domin bunƙasa tattalin arziki

Gwamna Okezie Ikpeazu na jihar Abia, ya bayyana takalmin da ya haɗa da hannunsa a matsayinsa na ɗalibin makarantar Aba-based Footwear Academy, kamar yadda dailytrust ta ruwaito.

KARANTA ANAN: Da Duminsa: Zamu Fitar da Dan Takarar Shugaban Kasa a 2023 Wanda Kowa Zai Kaunace Shi, APC

A wata fira da gwamnan yayi da manema labarai, ya nuna takalmin sandal da ya haɗa dakansa yayin da yake murmushi a fuskarsa.

Gwamna Okezie Ikpeazu
Hotunan Wani Gwamna da Ya Rungumi Sana'ar Hada Takalmi da Takalman da Yake Haɗawa Hoto: dailytrust.com
Asali: UGC

Gwamna Ikpeazu ya sanar da shiga makarantar koyon haɗa takalman sanyawa a watan Mayun da ya gabata.

Gwamna ya yi kira ga yan Najeriya su yi koyi da shi

Kara karanta wannan

Tsamo Ƴan Nigeria Miliyan 100 Daga Ƙangin Talauci: Har Yanzu Bamu Makara Ba – Buhari

Bayan shigarsa makarantar, gwamnan ya yi kira ga yan Najeriya da su ɗauki kayan da ake haɗawa a ƙasa da muhimmanci kuma su rinka amfani da su domin hanya ce ta bunƙasa tattalin arziki.

KARANTA ANAN: Yanzu-Yanzu: Yan Bindiga Sun Hallaka Jariri Dan Wata Uku Tare da Mutane da Dama a Benuwai

Ya bayyana cewa tun sanda ya karɓi ragamar mulkin jihar a 2015, kayan da yake sanyawa da takalmansa duk a Najeriya ake yinsu.

"Tun da na karɓi mulki, kayana da takalman da nake sanyawa a cikin ƙasar mu aka haɗa su," inji Gwamnan.

Hotunan gwamnan ɗauke da takalmin

Gwamnan Abia, Okezie Ikpeazu
Hotunan Wani Gwamna da Ya Rungumi Sana'ar Hada Takalmi da Takalman da Yake Haɗawa Hoto: dailytrust.com
Asali: UGC

Gwamnan Abia, Okezie Ikpeazu
Hotunan Wani Gwamna da Ya Rungumi Sana'ar Hada Takalmi da Takalman da Yake Haɗawa Hoto: dailytrust.com
Asali: UGC

A wani labarin kuma Barka da Sallah: Shugaba Buhari Ya Gwangwaje Yan Bautar Kasa NYSC da Kyautar Kudi da Shanu a Daura

Shugaba Buhari ya baiwa matasa yan bautar ƙasa dake aiki a Daura kyautar kuɗi, shanu da buhunan shinkafa.

Buhari ya nuna jin daɗinsa da ziyarar barka da sallah da matasan suka kai masa har gida, ya kuma roke su da su zama jakadu nagari.

Kara karanta wannan

Babbar Sallah: Ku Kara Hakuri Yayin da Muke Kokarin Inganta Rayuwarku, Shugaba Buhari Ga Yan Najeriya

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262