Jiragen Yaki 'Super Tucano' Guda 6 Sun Baro Amurka, Zasu Iso Najeriya Ba da Jimawa Ba, NAF

Jiragen Yaki 'Super Tucano' Guda 6 Sun Baro Amurka, Zasu Iso Najeriya Ba da Jimawa Ba, NAF

  • Rundunar sojin sama NAF ta tabbatar da cewa jiragen yaƙin super tucano guda shida sun baro Amurka
  • A wani jawabi da kakakin NAF ya fitar, yace jiragen zasu biyo ta wasu ƙasashe biyar kafin isowar su
  • Yace an gama shirye-shirye ƙaddamar da su da zaran sun iso Najeriya, za'a sanar da haka nan gaba

Kashin farko na jiragen yaƙin 'A-29 Super Tucano' sun baro haɗaɗɗiyar ƙasar Amurka, suna kan hanyarsu ta zuwa Najeriya.

KARANTA ANAN: Cikakken Bayani: NAFDAC Ta Amince da Sabbin Rigakafin COVID19, Ta Faɗi Amfani da Hatsarinsu

Kakakin rundunar dakarun sojin sama, NAF, Edward Gabkwet, shine ya bayyana haka a wani jawabi da ya fitar ranar Alhamis a shafn sada zumunta na facebook.

yace jiragen sun baro ƙasar Amurka ranar Laraba, kuma ana tsammanin isowar su Najeriya a kowane lokaci.

Yace: "Kashin farko na Jiragen yakin super tukano guda 6 sun baro Amurka jiya Laraba 14 ga watan Yuli, suna kan hanyar zuwa Najeriya."

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Bayan Cece-Kuce, Sanatoci Sun Amince da Naɗin Wani Kwamishinan Zaɓe, INEC

Jirgin yaƙi
Sabbin Jiragen Yaki 'Super Tukano' Guda 6 Sun Baro Amurka Zuwa Najeriya Hoto: premiumtimesng.com
Asali: UGC

"Jiragen shida zasu keto ƙasashen biyar da suka haɗa da, Canada, Greenland, Iceland, Spain da Algeria kafin su iso Najeriya a ƙarshen watan Yuli 2021."

"An shirya bikin ƙaddamar da jiragen zuwa cikin kayan aikin rundunar sojin sama a hukumance jim kaɗan bayan isowarsu a watan Agusta 2021, kuma za'a sanar a lokacin da ya dace."

Gwamnatin tarayya ta siyo jirage 12

A watan Fabrairun da ya gabata ne, gwamnatin tarayya ta siyo jiragen 'Super Tucano' guda 12 akan kuɗi $496 miliyan.

A baya, an sha sanar da ranakun isowar kashin farko na jiragen, kafin wannan sanarwar ta yau Alhamis.

Gwamnati na fatan jiragen zasu taimakawa sojoji a yaƙin da suke yi da yan ta'adda a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

KARANTA ANAN: Da Dumi-Dumi: Bayan Cece-Kuce, Sanatoci Sun Amince da Naɗin Wani Kwamishinan Zaɓe, INEC

Legit.ng hausa ta tattaro muku wasu daga cikin ra'ayoyin yan Najeriya dangane da wannan labarin.

Kara karanta wannan

Da dumi-dumi: Rikici ya barke a zauren majalisa kan batun masana'antar man fetur

Dondo Dagba, yace:

"Wai meyasa ba zaku iya boye irin wannan cigaban bane, kubar waɗannan yan ta'adda da yan bindigan cikin duhu? wannan na nuni da cewa kuna kasuwancin ku ne ba wani abu ba."

Gift-tony Nwaozuzu, yace:

"Ina mamakin meyasa muke bayyana komai a ƙasar nan har da waɗanda bai kamata ba. Ina da tambaya, shin haka ƙasar Amurka suke yi idan sun sayi abu ga sojojin su? gaskiya ya kamata mu gane."

A wani labarin kuma EFCC Ta Kaddamar da Manhajar Tona Asirin Masu Cin Hanci da Rashawa a Najeriya

Hukumar EFCC ta ƙaddamar da sabuwar manhajar bankaɗo bayanan masu aikata cin hanci a Najeriya.

Shugaban hukumar ya bayyana yadda yan Najeriya zasu tura bayanai da hotunan masu aikata laifin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262