Da dumi-dumi: PDP ta nada sabon mataimakin bulaliyar majalisar dattawa

Da dumi-dumi: PDP ta nada sabon mataimakin bulaliyar majalisar dattawa

  • Sauya sheka da Sanata Sahabi Ya'u ya yi zuwa jam'iyyar All Progressives Congress a Zamfara ya sanya PDP ta yi sabon nadi
  • Jam’iyyar adawar a ranar Alhamis, 15 ga watan Yuli, ta zabi sabon mataimakin bulaliyar majalisar dattawan Najeriya
  • Sabon wanda aka nada shi ne Sanata Ibrahim Abdullahi Danbaba wanda ke wakiltar yankin Sokoto ta Kudu

Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a ranar Alhamis, 15 ga watan Yuli, ta nada Sanata Ibrahim Abdullahi Danbaba a matsayin sabon mataimakin bulaliyar majalisar dattawa.

Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan ne ya karanta wasikar nadin Danbaba a ranar Alhamis, 15 ga watan Yuli, a zauren majalisar.

KU KARANTA KUMA: Jama’a sun fusata yayin da gwamnatin jihar Taraba ta fara siyar da fom din daukar aiki

Da dumi-dumi: PDP ta nada sabon mataimakin bulaliyar marasa rinjaye a majalisar dattawa Hoto: Peoples Democratic Party
PDP ta nada Sanata Danbaba a matsayin sabon mataimakin bulaliyar marasa rinjaye a majalisar dattawa Hoto: Peoples Democratic Party
Asali: Facebook

Wasikar da aka ambata tana dauke da sanya hannun sakataren jam'iyyar adawa ta kasa, Ibrahim Tsuari, jaridar The Nation ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Ta’addanci: Mataimakin gwamnan Zamfara ya shiga gagarumin matsala bayan gangamin PDP

Sabon wanda aka nada, mai wakiltar yankin Sokoto ta Kudu a majalisar dattawa, ya cike mukamin magabacinsa, Sanata Sahabi Ya’u, wanda ya sauya sheka zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

KU KARANTA KUMA: Yanzu-Yanzu: Shugaba Buhari ya dira Zawaciki, jihar Kano

Matawalle: PDP ta ce lallai sai an rantsar da mataimakin gwamnan Zamfara a matsayin gwamna

A wani labari na daban, jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta ce tana nan kan matsayinta na cewa sai an rantsar da mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Mahdi Aliyu Gusau a matsayin gwamnan jihar.

A cewar jam'iyyar adawar, gwamna Bello Matawalle ya rasa damar zama a kujerar a daidai lokacin da ya sauya sheka zuwa jam'iyyar All Progressives Congress (APC), Daily Nigerian ta ruwaito.

Legit.ng ta tattaro cewa PDP ta sake jaddada matsayinta game da rikicin na Zamfara a cikin wata sanarwa daga kakakinta, Kola Ologbondiyan.

Kara karanta wannan

Matawalle: PDP ta ce lallai sai an rantsar da mataimakin gwamnan Zamfara a matsayin gwamna

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng