Sunaye: Gimbiya da dan shekara 1 daga cikin iyalin sarkin Kajuru dake hannun 'yan bindiga

Sunaye: Gimbiya da dan shekara 1 daga cikin iyalin sarkin Kajuru dake hannun 'yan bindiga

  • Bayan sa'o'i ashirin da hudu da sace Sarkin Kajuru, 'yan bindiga sun sako shi
  • Sai dai sarkin kadai suka sako yayin da suka rike sauran mutane 13 da suka sata
  • Daga cikin mutum goma sha ukun akwai gimbiya 1 tare da yaro mai shekara 1 a duniya

Bayan sa'o'i ashirin da hudu da sace Sarki Alhaji Alhassan Adamu na Kajuru, 'yan bindiga sun sako shi tare da mika shi ga iyalinsa.

A ranar Lahadi, wasu miyagun 'yan bindiga sun shiga har cikin gidan sarautar Kajuru inda suka sace sarki tare da wasu mutum 13.

Sai dai 'yan biindigan sun sako sarkin tare da rike gimbiya daya da sauran wadanda suka sace, Daily Trust ta ruwaito.

KU KARANTA: Hotuna da bidiyon Ahmed Musa tare da dalleliyar sabuwar amaryarsa sun bayyana

Sunaye: Gimbiya da 'yar shekara 1 daga cikin iyalin sarkin Kajuru dake hannun 'yan bindiga
Sunaye: Gimbiya da 'yar shekara 1 daga cikin iyalin sarkin Kajuru dake hannun 'yan bindiga. Hoto daga dailytrust.com
Asali: UGC

KU KARANTA: Dalla-dalla: Gagarumin Luguden Wuta na Sa'a 1 aka yi Kafin Sace Sarkin Kajuru

Daga cikin wadanda 'yan bindigan suka rike akwai gimbiya, diyar sarkin guda daya mai suna Zainab da kuma yaro karami mai shekara daya kacal a duniya.

Kara karanta wannan

Yariman Kajuru ya bayyana abinda 'yan bindiga suka sanar masa kafin sakin mahaifinsa

Ga jerin sunayen wadanda har yanzu ke hannun 'yan bindigan:

Zainab Alhassan (diyar sarki)

Zainab Mukhtar, (jika)

Muhammad Sa’adanu (jika)

Salim Musa (jika)

Faisal Musa (jika)

Ahmed Mukhtar (jika)

Suleiman Umar (Mai sarauta)

Nazifi Rayyanu

Ayuba Yunusa

Amina Abubakar

Maryam Abubakar

Mardiyya Sani

Mudassir Sani (yaro mai shekara 1)

'Yan bindiga sun bada hakuri

Kamar yadda daya daga cikin wadanda suka karbo sarkin ya bayyana, ya ce miyagun 'yan bindigan sun kira su kan su zo su karba sarkin da yammaci,

Bayan isarsu, sun samu 'yan bindiga dauke da makamai kuma sanye da kayan sojoji inda suka dinga bada hakuri kan abinda suka yi.

'Yan bindigan sun tabbatar da cewa basu samu natsuwa da kwanciyar hankali ba tun bayan da suka saci basaraken a ranar Lahadi, Daily Trust ta wallafa.

A wani labari na daban, Gwamna Babagana Zulum na jihar Borno ya musanta rahoton dake yawo na nada gwamna a wasu yankunan jihar Borno da Boko Haram tare da ISWAP suka yi.

Kara karanta wannan

Cikakken Bayani: Yan Bindiga Sun Sako Sarkin Kajuru, Sun Cigaba da Rike Iyalansa

A makon da ya gabata, bidiyon da ake zargin na nada gwamnan Boko Haram a Borno ne ya dinga yawo a kafafen sada zumuntar zamani, Daily Trust ta ruwaito.

Hukumar rikon kwarya ta 'yan ta'addan ta samu shugabancin wani Abba Kaka, wanda aka nada a matsayin shugaban wasu yankunan Borno.

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel