Da Ɗumi-Ɗumi: El-Rufa'i Ya Tabbatar da Mutuwar Tsohon Mataimakin Gwamnan Kaduna
- Gwamna El-Rufa'i na jihar Kaduna, ya tabbatar da mutuwar tsohon mataimakinsa , Bantex
- Gwamnan ya bayyana marigayin a matsayin ɗan uwansa kuma abokin gwagwarmaya
- Yace gwamnati da jama'ar jihar Kaduna za su yi matuƙar kewarsa, saboda ƙoƙarinsa na kawo cigaba
Gwamna Malam Nasiru El-Rufa'i na jihar Kaduna, ya tabbatar da mutuwa tsohon mataimakin gwmanan jihar, Barbanas Bala Bantex, kamar yadda vanguard ta ruwaito.
KARANTA ANAN: Bayan Yan Bindiga Sun Sace Sarkin Kajuru, Shugaban Majalisa Ya Yi Zazzafan Martani
El-Rufa'i ya bayyana cewa a wurinshi ya rasa babban aboki kuma abokin aiki a wajen kawo cigaban jihar Kaduna.
Gwamnan, a wani jawabi ɗauke da sanya hannunsa, yace yana cikin wani yanayi mai wahala yayin da ya samu labarin mutuwar abokinsa kuma ɗan uwansa, Barnabasa Yusuf Bala (Bantex).

Asali: UGC
Gwamnan Yace: "Tun sanda muke karatun jami'a a shekarar 1970 zuwa sanda muka zama abokan aiki a gwamnatance, Bantex ya kasance mai dogaro da kanshi kuma mutum ne mai basira sosai."

Kara karanta wannan
Bayan Yan Bindiga Sun Sace Sarkin Kajuru, Shugaban Majalisa Ya Yi Zazzafan Martani
"Tare da shi muka yi gwagwarmayar kawo canji a jihar Kaduna a 2015. A zangon mulkin mu na farko yayi amfani da dukkan basirar sa wajen kawo cigaba a Kaduna lokacin yana mataimakin gwamna."
Kaduna za ta yi kewar Bantex
Malam El-Rufa'i ya ƙara da cewa marigayin ya yi aiki da dama don kawo cigaba a Kaduna tun kafin ya zama mataimakin gwamna bayan zaɓen 2015.
Yace marigayin ya riƙe muƙamin shugaban ƙaramar hukumar Ƙaura, sannan ya shiga majalisar dokokin jihar Kaduna a matsayin mai wakiltar ƙaramar hukumar ƙaura, kamar yadda the nation ta ruwaito.
KARANTA ANAN: Illar COVID19: Yadda Magidanta a Najeriya Ke Fama da Hauhawar Farashin Kayan Abinci, Duk da Ƙarancin Kuɗin Shiga
Yace: "Zamu yi kewarsa sosai, basirarsa da ƙoƙarinsa wajen kawo cigaba a Kaduna."
"Na yi magana da iyalansa, kuma na musu ta'aziyya a madadin gwamnatin Kaduna da al'ummar jihar baki ɗaya."
"Zamu yi aiki tare da iyalansa wajen ganin mun yi bankwana da mutumin da ya ke tunanin mu har a lokacin da ba shi da lafiya."
A wani labarin kuma Shugaba Buhari Ya Yi Martani Kan Harin Zamfara da Kaduna, Ya Umarci Dakarun Soji Su Murkushe Yan Ta'adda
Shugaba Buhari ya yi Allah wadai da hare-hare da aka kai kwanan nan jihar Zamfara da Kaduna.
Shugaban ya umarci sojoji da su ɗauki matakin murkushe duk wasu yan ta'adda ta yaren da zasu fahimta.
Asali: Legit.ng