Da dumi-dumi: Manyan shugabannin PDP na kudu maso gabas sun koma APC, an saki sunaye

Da dumi-dumi: Manyan shugabannin PDP na kudu maso gabas sun koma APC, an saki sunaye

  • Shugabannin jam’iyyar People Democratic Party (PDP) a kudu maso gabas suna yada zango a jam’iyyar APC gabanin zaben 2023
  • Kimanin mambobin jam’iyyar adawa uku ne suka koma jam’iyya mai mulki a ranar Juma’a, 9 ga watan Yuli, a jihar Abia
  • Masu sauya shekar sun koma jam’iyyar APC tare da wani tsohon dan takarar gwamna na SDP a jihar

Manyan mambobin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a Abia a ranar Juma’a, 9 ga watan Yuli, sun sanar da sauya shekarsu zuwa jam’iyyar All Progress Congress (APC).

Daga cikin wadanda suka sauya sheka zuwa jam’iyya mai mulki harda tsohon dan takarar gwamna na Social Democratic Party (SDP), Honarabul Blessing Nwagba, jaridar Nigerian Tribune ta ruwaito.

KU KARANTA KUMA: Kungiyoyin Arewa sun gindaya wa kudu sharadin samun shugabancin kasa a 2023

Da dumi-dumi: Manyan shugabannin PDP na kudu maso gabas sun koma APC, an saki sunaye
APC ta sake samun karfi a jihar Abia Hoto: All Progressives Congress
Asali: Facebook

Tsoffin jiga-jigan PDP da suka yanke hukuncin a ranar Juma’a su ne Arch Anagha Mba, Cif Silvanus Nwaji, Barr Chibuike Nwokeukwu (SAN), jaridar Guardian ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Kungiyoyin Arewa sun gindaya wa kudu sharadin samun shugabancin kasa a 2023

Mutanen uku sun yi wa APC alkawarin za su yi aiki tukuru don tabbatar da nasarar ta a zaben gwamna na 2023 a Abia.

KU KARANTA KUMA: An harbe wani dan siyasar Najeriya har lahira a wajen taron APC a Lagas

PDP ta sake rasa ɗan majalisar tarayya bayan ya koma APC

A wani labarin, Jonathan Gaza, ɗan majalisar wakilai na tarayya, ya fice daga jam'iyyar Peoples Democratic Party, PDP, ya koma All Progressives Congress, APC, Premium Times ta ruwaito.

Mr Gaza ne ɗan majalisar PDP na ƙarshe daga jihar Nassarawa a majalisar kafin ya koma APC a ranar Laraba.

Premium Times ta ruwaito cewa gwamnan jihar Nassarawa, Abdullahi Sule ya tafi majalisar domin halartar sauya sheƙan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng