Da dumi-dumi: Shugaba Buhari ya yi sabon nadi mai muhimmanci

Da dumi-dumi: Shugaba Buhari ya yi sabon nadi mai muhimmanci

  • Shugaba Buhari ya amince da nadin Adamu Mohammed Abdulhamid a matsayin jakadan Najeriya a Kungiyar Kasuwanci ta Duniya
  • An tattaro cewa nadin nasa zai shafe tsawon shekaru hudu
  • Abdulhamid ya kasance jagoran yakin neman zaben Ngozi Okonjo-Iweala a Geneva wanda ya taimaka kwarai da gaske wajen zamantowarta babbar darakta ta WTO

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Adamu Mohammed Abdulhamid a matsayin jakadan Najeriya a Kungiyar Kasuwanci ta Duniya (WTO).

An sanar da sabon nadin da aka yiwa Abdulhamid, wanda zai shafe tsawon shekaru hudu, a cikin wata wasika daga ofishin shugaban ma’aikatan Shugaba Buhari, Ibrahim Gambari, kamar yadda jaridar Leadership ta ruwaito.

KU KARANTA KUMA: Kaduna: CP ya bayyana yadda ‘yan bindiga suka farma makarantu 5, suka sace dalibai 204 a cikin watanni shida

Da dumi-dumi: Shugaba Buhari ya yi sabon nadi mai muhimmanci
Shugaba Buhari ya amince da nadin Adamu Mohammed Abdulhamid a matsayin jakadan Najeriya a Kungiyar WTO Hoto: Femi Adesina
Asali: Facebook

Kafin sabon nadin nasa, Abdulhamid ya yi aiki a matsayin Shugaban riko / mai kula da harkokin Ofishin Kasuwancin Najeriya a WTO, Geneva, Switzerland.

Kara karanta wannan

Waiwaye: Bidiyon Shagari yana kunna sigari lokacin da Firayim Minista Tafawa Balewa ke jawabi ga taron jama'a

Ya kuma kasance jagoran yakin neman zaben Ngozi Okonjo-Iweala a Geneva wanda ya taimaka kwarai da gaske wajen zamantowarta babbar darakta ta WTO.

KU KARANTA KUMA: An harbe wani dan siyasar Najeriya har lahira a wajen taron APC a Lagas

Jakadan ya sami MSC a fannin Tattalin Arziki da Ci Gaban Kasa da Kasa daga Jami'ar Clemont Ferrand, Faransa, ya yi digirinsa na biyu a kan Gudanar da Harkokin Kasuwanci da Shugabanci daga Makarantar London Graduate School, Burtaniya; takardar shaida na alaƙar ƙasa da diflomasiyyar tattalin arziki daga Jami'ar Commonwealth, Landan.

Kungiyoyin mata sun kai karar Buhari a kotu, sun ce gwamnatin tarayya ta ware su a gefe

A wani labarin, jaridar Punch ta ce gamayyar kungiyoyin mata sun shigar da karar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari a gaban wani kotun tarayya a Abuja.

Kungiyoyin su na ikirarin cewa gwamnatin da Muhammadu Buhari yake jagoranta, ba ta yi da mata.

Kara karanta wannan

Matasan Sakkwato sun mamaye fadar Sarkin Musulmi akan kalaman batanci ga Annabi

A wannan kara da kungiyoyin suka shigar, sun bukaci kotu ta hana shugaban Najeriyar cigaba da saba ka’idar da ta ce a ba mata 35% na mukaman gwamnati.

Asali: Legit.ng

Online view pixel