Bayan Matawalle, Jam'iyyar PDP Ta Faɗi Babban Dalilin da Yasa Gwamnoni Ke Ficewa Daga Cikinta

Bayan Matawalle, Jam'iyyar PDP Ta Faɗi Babban Dalilin da Yasa Gwamnoni Ke Ficewa Daga Cikinta

  • Wani jigon babban jam'iyyar hamayya PDP ya bayyana ainihin dalilin da yasa gwamnoni ke guduwa daga jam'iyyar
  • A cewarsa duk gwamnan da ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC to ba shi da dalilin yin hakan
  • Sai-dai PDP ta zargi wasu daga cikin yan APC da yi musu maƙarƙashiya da tilastawa gwamnonin sauya sheƙa

Wani jigo kuma babba daga cikin yan majalisar zartarwa a jam'iyyar PDP yace jam'iyyarsu ba zata iya cewa komai ba dangane da sauya sheƙar gwamnan Zamfara, Bello Matawalle, kamar yadda leadership ta ruwaito.

KARANTA ANAN: Wata Sabuwa: Obasanjo Ya Sake Yin Magana a Kan Jita-Jitar An Sauya Buhari da Jibrin Sudan

Yace jam'iyyar PDP ba ta da ikon da zata hana gwamnan komawa jam'iyya mai mulki wato APC

Sai-dai ya ƙara da cewa Matawalle bai faɗawa PDP dalilinsa na ficewa daga cikinta ba, amma akwai wasu daga cikin yan APC dake matsawa gwamnoni su sauya sheƙa.

Dalilin da yasa gwamnoni ke ficewa daga PDP
Bayan Komawar Matawalle APC, Jam'iyyar PDP Ta Faɗi Babban Dalilin da Yasa Gwamnoni Ke Ficewa Daga Cikinta Hoto: vanguardngr.com
Asali: UGC

Jigon a PDP yace: "Matsayar mu itace ba zamu ce komai ba gane da ficewarsa, kuma ba zamu ɗauki wani mataki a kan haka ba."

"Har zuwa yanzun gwamnan bai faɗa mana dalili da yasa ya fice daga jam'iyyar mu ba, kuma baida wani dalili na cewa an mishi ba dai-dai ba."

Gwamnonin basu da hujjar ficewa daga PDP

Ya cigaba da cewa: "Gwamna Ben Ayade na jihar Cross Rivers, wanda ya koma APC, har yanzun bai faɗa mana abinda PDP ta masa wanda ba dai-dai ba."

"Hakazalika, gwamna Dev Umahi na jihar Ebonyi, da yake ta kuka cewa ana rashin adalci a PDP, har yanzun ya gaza amsa mana tambayar mu cewa a ina ake rashin adalcin."

KARANTA ANAN: Ba Gudu Ba Ja da Baya a Matakin Mu Na Korar Ma'aikata, El- Rufa'i Ya Faɗawa Buhari

Babban jigon PDP ɗin yace akwai wasu mutane a cikin jam'iyyar APC dake jan hankalin gwamnonin na su koma jam'iyyar su.

A cewarsa, duk wanda ya yanke cewa zai fice daga jam'iyyar mu, bamu da ikon hana shi.

A wani labarin kuma APC Ta Shirya Babban Gangami Yayin da Jiga-Jiganta Zasu Dira Jihar Zamfara

Jam'iyyar APC ta shirya babban gangami na musamman ranar Talata domin tarbar gwamnan Zamfara, Matawalle, kamar yadda punch ta ruwaito.

Ana sa ran jiga-jigan jam'iyyar na ƙasa da na jihar Zamfara ne zasu tarbi gwamnan tare da yan majlisar dokokinsa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel