Yan bindiga sun sake kai hari garuruwan Neja, sun kashe mutane da dama

Yan bindiga sun sake kai hari garuruwan Neja, sun kashe mutane da dama

- Yan bindiga sun kai farmaki wasu kauyuka da ke yankin Kwata a karamar Hukumar Wushishi da ke Jihar Neja

- Lamarin ya afku ne a ranar Juma'a, 28 ga watan Mayu, inda aka kashe akalla mutane 14

- Maharan sun kuma yi garkuwa da wasu mutane da dama

Akalla mutane 14 ne aka ba da rahoton sun mutu biyo bayan hare-haren da ‘yan bindiga suka kai a wasu kauyuka da ke yankin Kwata a karamar Hukumar Wushishi da ke Jihar Neja, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Wadanda lamarin ya rutsa da su sun hada da mata da kananan yara wadanda ke kokarin tsiratar da rayukansu yayin harin.

An tattaro cewa wasu sun gudu zuwa cikin kogi don tserewa daga harin amma abun bakin ciki sai suka nitse.

Yan bindiga sun sake kai hari garuruwan Neja, sun kashe mutane da dama
Yan bindiga sun sake kai hari garuruwan Neja, sun kashe mutane da dama Hoto: Daily trust
Asali: UGC

KU KARANTA KUMA: 2023: Hotuna Sun Nuna Yadda Tinubu Ya Tarbi Atiku a Filin Jirgin Sama Yayinda Ya Dawo Daga Dubai

Jaridar Thisday ta ruwaito cewa yan fashin wadanda suke da yawa sun fara gudanar da ayyukansu ne a tashar jirgin kasa ta Akeri inda suka kashe mutum daya kafin su kai harin zuwa kasuwar kifi.

Majiyoyi daga yankin sun ce ana ci gaba da gano gawarwakin wadanda aka kashe tare da binne su yayin da wasu da dama suka bata.

An kuma tattaro cewa yan fashin sun harbe mutane bakwai inda mutum hudu daga cikin su aka tabbatar da sun mutu yayin da wasu biyu ke karbar magani a asibitin kwararru na IBB, Minna.

Gaba daya dukka, an ce mutane 14 ne suka rasa rayukansu yayin da garin ke ci gaba da ƙididdigar asarar da suka yi kamar yadda wasu iyalai suka ce ba su ga yan uwansu da danginsu ba.

'Yan fashin sun kuma yi awon gaba da shanu da dama, sun kwace babura tare da yin garkuwa da mutane, musamman' yan mata.

Gidaje sun watse sun zama kufai

An tattaro cewa mazauna kauyukan yankin sun bar gidajensu kuma daruruwan mutane sun koma garin Wushishi a yanzu haka.

Mutanen yankin sun zargi hukumomi da yin komai don taimaka masu.

Sun ce, Tabbas, har zuwa wannan lokacin ba wani kokarin da gwamnati da jami’an tsaro suka yi don kare lafiyar mutane ko bayar da kowani agaji ga ‘yan gudun hijirar.
A yanzu haka ‘yan fashin suna kusa da kauyukan a hanyar Tashan Jirgin Wushishi zuwa Kundu a karamar hukumar Rafi.
Abun tsoro yanzu shine ayyukan yan fashin na iya shafar kauyuka da fasinjojin da ke bin hanyar.

KU KARANTA KUMA: Hatsarin jirgin soji: NAF ta bayyana dalilin da yasa aka kyale kananan matuka suna jigila da COAS da sauransu

A wani labarin, fusatattun matasa sunyi zanga-zanga kan irinsu kisan awakin da yan bindiga ke musu a karamar hukumar Zurmi ta jihar Zamfara.

Wannan fushi ya kaisu ga banka wuta fadar Sarkin Zurmi.

Bidiyon da TVCNews ta samu ya nuna yana wasu matasa ke kona wasu sashen fadar.

Asali: Legit.ng

Online view pixel