NBS ta fitar da jerin basusukan da ake bin kowace jihar Najeriya yayin da ya kai N4.2tn

NBS ta fitar da jerin basusukan da ake bin kowace jihar Najeriya yayin da ya kai N4.2tn

- Hukumar kididdiga ta kasa ta fitar da bayanan bashin da ake bin kowace jiha

- A cewar NBS, Legas ce jihar da ta fi kowacce bashi a kasar

- A halin yanzu, jihar Jigawa ce ke da mafi karancin bashi a kasa

Ana bin jihohin Najeriya ciki har da Babban Birnin Tarayya bashin N4.2tn a cewar Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS).

Da wannan sabon rahoto, Jihar Legas ce ke da kaso 12.15 na bashin har zuwa karshen 2020 yayin da jihar Jigawa ke da mafi karancin bashin a wannan rukuni da kashi 0.74 bisa dari.

KU KARANTA KUMA: 'Yan Najeriya sun kirkiri fasahar bin diddigin 'yan bindiga a duk inda suke

NBS ta fitar da jerin basusukan da ake bin kowace jihar Najeriya yayin da ya kai N4.2tn
NBS ta fitar da jerin basusukan da ake bin kowace jihar Najeriya yayin da ya kai N4.2tn Hoto: @Jidesanwoolu, @seyiamakinde
Asali: Twitter

Ga jerin jihohin da bayanan bashin su na yanzu.

Abia - N89.12bn (2.13 per cent)

Adamawa - N98.9bn (2.36 per cent)

Akwa Ibom - N230.8bn

Anambra - N59.97bn

Bauchi - N102.8bn

Bayelsa - N144.13bn

Benue - N126.12bn

Borno - N89.05bn

Cross River - N163.16bn,

Delta - N248.45bn

Ebonyi - N44.21bn

Edo - N80.78bn

Ekiti - N84.97bn

Enugu - N68.09bn

Gombe - N84.72tn

Imo - N150.2bn

Jigawa - N30.97bn

Kaduna - N68.75bn

Kano - N116.93bn

Katsina - N48.03bn

Kebbi - N56.81bn

Kogi - N68.09bn

Kwara - N63.63bn

Lagos - N508.78bn

Nasarawa - N59.4bn

Niger - N66.77bn

Ogun - N153.49bn

Ondo - N74.66bn

Osun - N134.11bn

Oyo - N94.5bn

Plateau - N137.8bn

Rivers - N266.9bn

Sokoto - N42.36bn

Taraba - N106.04bn

Yobe - N54.87bn

Zamfara - N98.02bn

FCT - N69.5bn

KU KARANTA KUMA: Ina shirin mayar da rundunar sojin Najeriya mai matukar karfin iko, Attahiru

A wani labarin, babban jagoran jam’iyyar APC mai mulki, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya bada shawarar yadda za ayi maganin fatara, a farfado da tattalin Najeriya.

Jaridar Daily Trust ta rahoto Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya na cewa ya kamata gwamnatin tarayya ta saki kudi da nufin yakar talauci da rashin aikin yi.

Bola Tinubu ya ce akwai bukatar shugabanni masu rike da madafan iko da ‘yan majalisa su hada-kai, a samu a ga yadda za a kawar da talaucin da ake fama da shi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel