Labari mai dadi: Gwamnatin Najeriya za ta gina kamfanin takin zamani na dala biliyan 1.3

Labari mai dadi: Gwamnatin Najeriya za ta gina kamfanin takin zamani na dala biliyan 1.3

- Gwamnatin Najeriya za ta kaddamar da sabon kamfanin sinadarin amoniya da kuma takin zamani da aka gina kan kudi sama da dala biliyan 1.3

- Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tabbatar da hakan a ranar Alhamis, 25 ga watan Maris

- Tuni dai gwamnatin tarayya da na kasar Moroko suka kulla yarjejeniya a kan haka

Gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari na shirin kaddamar da sabon kamfanin sinadarin amoniya da takin zamani wanda aka gina a kan kudi fiye da dala biliyan daya.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Twitter ta @MBuhari a ranar Alhamis, 25 ga watan Maris, yana mai cewa gwamnatinsa za ta gina masana’antar da hadin gwiwar kasar Moroko.

KU KARANTA KUMA: Kano: Dole 'yan siyasa su nuna shaidar biyan Zakka kafin su tsaya takara

Labari mai dadi: Gwamnatin Najeriya za ta gina kamfanin takin zamani na dala biliyan 1.3
Labari mai dadi: Gwamnatin Najeriya za ta gina kamfanin takin zamani na dala biliyan 1.3 Hoto: @MBuhari
Asali: Twitter

Buhari ya wallafa a shafin nasa cewa:

“Najeriya da Maroko sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya don samar da sinadarai na Dala biliyan 1.3 a Najeriya wanda zai samar da Ammonia da takin zamani daban-daban na NPK da DAP, ta hanyar amfani da iskar gas din Najeriya. Muna kan hanyarmu ta zama cibiyar samar da takin zamani na yanki.

“Sabon kamfanin idan aka kammala shi zai wadata kayayyakin da ake dasu na Dangote da Indorama wadanda ke samar da sinadarin urea da ammonia da sauran kayayyakin masana'antu. Waɗannan ƙari ne ga ɗimbin tsire-tsiren hada takin zamani da muka farfaɗo da su a ƙarƙashin shirin takin zamani na Shugaban kasa.

“Ina farin ciki da hadin gwiwa da goyon bayan kungiyar dillalai da masu samar da takin zamani ta Najeriya (FEPSAN), da kuma ci gaban da suka samu a cikin shekaru biyar da suka gabata. A yau, muna ganin fa'idodin shawarar da suka yanke mai kyau, na dogon lokaci.

KU KARANTA KUMA: Ta'addanci, sauyin yanayi, rashin tsaro, manyan kalubale ne garemu, Buhari

“Wani abun guda da ya cancanci yabo da ambato shine cewa duk jarin da FEPSAN ta saka sun daidaita tsakanin birane da ƙauyukan Najeriya. Waɗannan su ne nau'ikan saka hannun jari da ake buƙata don magance rashin aikin yi da matsalolin tsaro da al'ummarmu ke fuskanta a yau.

"Dole ne mu yi ƙoƙari na musamman don tabbatar da cewa ba a yi watsi da yankunan karkara na Najeriya ba. Dole a habbaka bangaren zuba hannun jari da samar da ayyukan yi.

"Yayin da muke ci gaba da fadada ayyukanmu na tsaro don kawo karshen wadannan matsalolin, yana da muhimmanci a lura cewa zaman lafiya da ci gaba za su dore ne kawai idan muka hada kai kuma muka ba da goyon baya ga saka hannun jari wanda ke ba da dama ga ’yan karkararmu."

A wani labarin, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya caccaki magajinsa, Abdullahi Umar Ganduje game da shirin da gwamnatinsa ke yi na ciyo bashin naira biliyan 20 domin aiwatar da aikin gina gada a birnin jihar.

A cewar Kwankwaso, hakan ba daidai bane ga gwamnati ta ciyo bashin da zai bar al’ummar da za a haifo nan gaba da gwagwarmayar biyan bashi.

A wata hira da yayi da sashin BBC, tsohon gwamnan ya ce gina gadar wadda ta hada birnin Kano da hanyar zuwa Wudil, hakki ne da ya rataya a kan wuyar gwamnatin tarayya.

Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai.

Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi.

Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara.

Don samun karin bayani a kan ta, ziyarci shafinta na Twitter @ AishaMu11512411

Asali: Legit.ng

Online view pixel