Kamar El-Rufai, gwamnan Kogi yace ba zai yi sasanci da 'yan ta'adda ba

Kamar El-Rufai, gwamnan Kogi yace ba zai yi sasanci da 'yan ta'adda ba

Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, yace gwamnatinsa ba za ta taba sasanci da 'yan ta'adda ba.

Ya sanar da hakan ne yayin tattaunawa da gidan talabijin na Channels a shirin siyasarmu a yau.

KU KARANTA: Mutum 101 da ake zargin 'yan Boko Haram ne suna maka FG a kotu, sun bukaci diyyar N303m

Kamar El-Rufai, gwamnan Kogi yace ba zai yi sasanci da 'yan ta'adda ba
Kamar El-Rufai, gwamnan Kogi yace ba zai yi sasanci da 'yan ta'adda ba. Hoto daga @Channelstv
Asali: Twitter

Karin bayani na nan tafe...

KU KARANTA: Yadda jiragen sama ke wurgawa 'yan bindiga makamai da abinci a Zamfara

A wani labari na daban, nan babu dadewa gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammed zai koma jam'iyyar APC, cewar gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum.

Gwamna Zulum ya sanar da hakan ne a ranar Talata yayin bikin saka harsashin sabon gagarumin gidan gwamnatin jihar Bauchi da zai lamushe N6.3 biliyan, Channels TV ta wallafa.

"Bari in sake nuna godiyata ga takwarana gwamnan jihar Bauchi da sauran takwarorina na arewa maso yamma da suke bani goyon baya mai matukar yawa."

Aisha Khalid ma'aikaciyar jaridar Legit.ng ce mai fatan shahara. Ta samu digirinta na farko a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a shekarar 2018.

Ta kwashe shekaru biyu tana rubutu a fannonin siyasa, nishadi, tsegumi da sauransu.

Za a iya bibiyar Aisha a shafinta na Twitter @DiyarKatsinawa

Asali: Legit.ng

Online view pixel