Ba kudin fansa 'yan bindiga suke nema ba kafin su sako daliban Kagara, in ji Sheikh Gumi

Ba kudin fansa 'yan bindiga suke nema ba kafin su sako daliban Kagara, in ji Sheikh Gumi

- Shehin malamin Islama Gumi ya bayyana abinda 'yan bindiga ke bukata su sako yaran Kagara

- Malamin yace ba wai kudin fansa suke bukata a basu ba, suna bukatar wani abune daban

- Ya kuma bayyana cewa atattaunawarsu babu batun biyan kudin fansa, babu wannan sharadin

Shehin malamin addinin Islama, Sheikh Gumi dake tattaunawa da 'yan ta'adda ya bayyana wasu daga cikin sharuddan da 'yan bindigar ke son a cika kafin su sako daliban Kagara da aka sace.

Shahararren malamin na arewa a wata hira da manema labarai, ya lura cewa tattaunawar ba ta kunshi biyan kudin fansa ba, PM News ta ruwaito.

A cewar Gumi, 'yan bindigar suna neman a saki 'yan uwansu da ke hannun jami'an tsaro.

“Suna da mutane hudu a tsare, kuma suna neman su. Suna kuma bukatar tabbaci kuma wannan shine dalilin da ya sa muke kira a yi musu afuwa. Sun dade suna fada; ya fi shekaru takwas," in ji Gumi.

KU KARANTA: Wani matashi ya dabawa tsohuwar budurwarsa wuka gaban kotu a jihar Adamawa

Ba kudin fansa 'yan bindiga suke nema ba kafin su sako daliban Kagara, in ji Sheikh Gumi
Ba kudin fansa 'yan bindiga suke nema ba kafin su sako daliban Kagara, in ji Sheikh Gumi Hoto: Premium Times
Asali: UGC

“Wadannan mutane suna gwagwarmayar wanzuwarsu ne saboda idan sun je gari ana kashe su idan 'yan sanda suka gan su a hanya, sai su kame; wani lokacin ana zartar musu da hukunci ba bisa ka'ida ba, don haka suka dauki makami ga jihar.

"Lokacin da kuka yi musu afuwa, dukkansu za su yar da makamansu.”

Shehin malamin addinin musuluncin ya kuma ce akwai yiwuwar za a saki daliban da aka sace yau Lahadi, tare da ci gaba da tattaunawa tsakanin wadannan barayin da gwamnati. Ya ce an samu jinkirin sakin saboda kayan aiki.

“Abin da na ji daga (wanda muka tuntube su) shi ne har yanzu suna tattaunawa don sakin su (‘yan makaranta da ma’aikata) kuma da fatan, da fatan, za mu same su gobe (Lahadi)" in ji shi.

“Har zuwa yanzu, ba su iya gano yaran ba, wadanda (suka yi satar). Kun san su kungiyoyin rabuwa ne.

"Don haka, lokacin da kuke ma'amala da ƙungiyoyi irin wannan a cikin yanki mai faɗi, ba tare da sadarwa ba, ba hanya, to dole ya zama na da jinkiri. Amma manyan su a shirye suke su tattauna kuma su dakatar da satar gaba daya.”

KU KARANTA:

A wani labarin, Shahararren malamin addinin Islama, Sheikh Gumi, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta ba 'yan fashi da ke son yin sulhu idan har za a magance matsalar tsaro a yanzu.

Malamin ya bayyana hakan ne a ranar Juma'a yayin ganawa da manema labarai a Minna, babban birnin jihar Neja.

Salisu Ibrahim, mai rubutu a masana'antar Legit.ng Hausa da ya fara aiki a baya-bayan nan. Ya kware wajen kawo rahotanni na siyasa, kimiyya, al'adu da sauran lamurran yau da kullum.

Ya yi karatun diploma a fannin karantar da turanci a jami'ar Ahmadu Bello, ya kuma karantar na tsawon shekaru 7.

A halin yanzu yana zangon karshe na karatun digiri a fannin ilimin fasahar sadarwa a International Open University.

Ku bibiyi shafinsa na twitter a @therleez

Asali: Legit.ng

Online view pixel