'Yan Najeriya sun tafka mummunan kuskuren zabar APC, in ji wani gwamna

'Yan Najeriya sun tafka mummunan kuskuren zabar APC, in ji wani gwamna

- Gwamnan jihar Ribas ya bayyana cewa 'yan Najeriya basu girbi alherin da suke tsammani a zabar APC ba

- Ya ce babban kuskure 'yan Najeriya suka yi da suka zabi jam'iyyar APC domin ta mulke su

- Gwamnan ya bayyana cewa yakamata 'yan Najeriya yanzu kam su hankalta su zabi jam'iyyar PDP

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike ya ba da tabbacin gazawar jam’iyyar APC wajen magance fitina, fashi da makami da cin hanci da rashawa zai tilastawa ‘yan Nijeriya su hambare jam’iyyar a shekarar 2023, The Nation ta ruwaito.

Wike ya lura da cewa, tare da matsalar tattalin arziki da ake ciki da kuma karuwar 'yan ta'adda, a bayyane yake cewa' yan Najeriya sun fahimci cewa sun yi mummunan kuskure da suka zabi APC.

Wata sanarwa da mataimakinshi na musamman kan harkokin yada labarai, Kelvin Ebiri ya fitar, ta ruwaito Wike yana fadar haka ne a ranar Alhamis.

KU KARANTA: Kwamacala: Wata mata ta rabu da saurayinta ta kuma auri kanta

'Yan Najeriya sun tafka mummunan kuskuren zabar APC, in ji wani gwamna
'Yan Najeriya sun tafka mummunan kuskuren zabar APC, in ji wani gwamna Hoto: BBC
Asali: UGC

Gwamnan ya fadi hakane jim kadan bayan duba babbar hanyar musaya da karkashin kasa da gwamnan Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri ke ginawa a Yola

Wike ya ce ya gamsu da irin ci gaban da Fintiri ya kawo, yana mai cewa irin wannan aikin ana yin sa a jihohin da Gwamnonin PDP ke mulki.

Gwamnan ya bayyana cewa da alama 'yan Najeriya ba su ji dadin yadda gwamnatin APC ta jagoranci ta tafiyar da al'amuran kasar ba.

Wike ya ce: “Shin 'yan Nijeriya suna farin ciki? Amsar ita ce a'a. Idan yan Najeriya basu ji daɗi ba, menene sakamakon da kuke niyyar samu? Babu shakka, 'yan Najeriya za su so gwamnatin APC ba za ta mulke su ba a shekarar 2023."

"Na yi imanin cewa 'yan Najeriya yanzu sun san cewa sun yi kuskure kuma suna so su gyara kuskuren ta hanyar zabar PDP ba APC ba," in ji shi.

KU KARANTA: Kotu tayi watsi da tuhumar EFCC na badakalar N900bn kan tsohon gwamna Yari

A wani labarin, Gwamna Simon Lalong na jihar Filato ya bukaci mambobin majalisar zartarwa ta jihar da su yi rajistar membobin da ke gudana da kuma sake jaddada zamansu 'yan jam’iyyar APC, domin su tsira da mukamansu, Daily Nigerian ta ruwaito.

Mista Lalong ya yi kiran ne a ranar Litinin lokacin da ya karbi bakuncin wakilan jam’iyyar zuwa jihar don atisaye.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel