Akwai shirin barkewar rikici na kabilanci da addini a wasu jihohi, DSS

Akwai shirin barkewar rikici na kabilanci da addini a wasu jihohi, DSS

- Hukumar tsaro ta farin kaya ta gargadi 'yan Najeriya kan shirin da wasu suke yi na tada hankali

- Hukumar ta ce akwai wasu mutane da kungiyoyi da suke shirin tayar da kayan baya

- Akwai yiyuwar tada rikici da hare-hare a wuraren ibada da wurare masu muhimmaci

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta sake ankarar da ‘yan Najeriya game da shirin da wasu mutane da kungiyoyi ke yi na haifar da rikicin kabilanci da addini a wasu sassan kasar.

Hukumar DSS a watan Junairu ta yi bayanin cewa wasu mutane suna aiki tare da mutanen waje don tayar da rikicin addini a fadin kasar.

Peter Afunanya, jami'in hulda da jama'a na hukumar DSS, a cikin wata sanarwa a ranar Laraba, ya ce sabon masaniyan da aka samu ya nuna matukar kokarin da wadannan kungiyoyin ke yi na gurgunta zaman lafiyar jama'a.

KU KARANTA: Abia: Muna biyan N100K kan duk wata saniya da aka kashewa makiyaya

Akwai shirin barkewar rikici na kabilanci da addini a wasu jihohin, DSS
Akwai shirin barkewar rikici na kabilanci da addini a wasu jihohin, DSS Hoto: Recruitment Gate
Asali: Facebook

Afunanya ya ce wadanda ake zargi da shirya makarkashiyar suna son “yin amfani da wasu lamuran kuskure” don yin barna a cikin kasar ta hanyar haifar da rikice-rikice tsakanin addinai.

Ya kuma bayyana cewa suna so su yi amfani da sojojin gona su kai hari kan wasu cibiyoyin bauta, shugabannin addinai, mutane gami da mahimman wurare masu rauni.

Ya ce mutanen da ake zargin sun ci gaba da yin tsokaci, maganganun rashin kiyayewa da rarraba kawunan 'yan kasa da juna don haifar da rikice-rikicen kabilanci da na addini.

"A karo na goma sha shida, Hukumar ta yi gargadi sosai ga mutane kan wadannan abubuwan da su hanzarta barin ayyukansu da suka (shirya) ko kuma su fuskanci fushin doka," in ji shi.

"DSS tare da hadin gwiwar sauran jami'an tsaro da jami'an tsaro za su dauki matakan da suka dace don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin 'yan kasa."

KU KARANTA: 'Yan fasa kwabrin shinkafar waje sun jikkata wasu jami'an Kwastam da wani soja

A wani labarin, 'Yan sanda a Abuja a ranar Talata, sun tabbatar da sace Mista John Makama, mahaifin Shugaban Karamar Hukumar Bwari, John Gabaya, The Nation ta ruwaito.

CSP Biodun Makanjuola, jami’in ‘yan sanda na shiyya (DPO), mai kula da ofishin 'yan sanda na Bwari, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata hira ta wayar tarho da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN).

Makanjuola ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 1:00 na rana a ranar Talata, ya kara da cewa ‘yan sanda na tattara bayanai kan hakikanin abin da ya faru.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel