Dukkan kasashen Afrika na bukatar shugaba irin Buhari

Dukkan kasashen Afrika na bukatar shugaba irin Buhari

- Shugaba Buhari ya sake jaddada bukatarsa ga shugabannin kasashen makwabta kan hadin kai

- Shugaban ya karbi bakoncin shugaban kasar Benin Patrice Talon a fadar shugaban kasa dake Abuja

- Shugaban ya bayyana dadlilin sa na ziyarce-ziyarce a zangon mulkinsa na farko

Shugaba Muhammadu Buhari a ranar Talata ya sake jaddada bukatar kasashen makwabta su kasance masu kiyaye muradun juna a koda yaushe, yana mai cewa dorewar juna ya dogara da juna, Vanugard News ta ruwaito.

Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne lokacin da yake karbar bakuncin shugaban kasar Benin, Patrice Talon, wanda ya kai ziyarar gani da ido a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Shugaban a cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai da yada labarai, Cif Femi Adesina ya fitar, ya ce:

“Kyakkyawar makwabtaka na da matukar muhimmanci a rayuwarmu. Rayuwar maƙwabcinka ma naka ne, kuma za mu ci gaba da aiki tare da maƙwabtanmu bisa wannan fahimtar.” yace

KU KARANTA: Sabuwar jam'iyyar siyasa mai karfi na nan zuwa, in ji Okorocha

Dukkan kasashen Afrika na bukatar shugaba irin Buhari
Dukkan kasashen Afrika na bukatar shugaba irin Buhari Hoto: Vanguard News
Asali: UGC

Ya tunatar da cewa a lokacin da ya hau mulki karo na farko a shekarar 2015, daya daga cikin matakan farko da ya dauka shi ne ziyartar kasashe makwabta na Chadi, Nijar, Kamaru da Benin.

Ya kuma bayyana ziyarar duk don samar da fahimtar juna kan batutuwa masu muhimmanci, da suka hada da tsaro, kasuwanci da ci gaba ya kaishi.

A cewarsa, “Kuma wadannan batutuwa ne da ya kamata mu ci gaba da tsunduma a kansu, domin amfanin kasashenmu da jama’armu. Duk wani abin da zai tayar mana da hankali dole ne a cire shi.”

Da yake magana a baya, Shugaba Talon ya ce, ya je Najeriya ne don nuna godiya ga Shugaba Buhari kan kyakkyawan shugabancin da yake nunawa a Najeriya da Afirka.

Da yake lura da cewa kalubalen shekarar 2020 suna da yawa, ya kuma jaddada cewa irin wannan kalubalen na iya kasancewa a shekarar 2021, “kuma dangantakarmu da makwabta dole ne, saboda haka, ta kasance mai kyau.

KU KARANTA: 2023: Manyan jiga-jigan APC sun ba Yahaya Bello da David Umahi shawarar tsayawa takaran shugaban kasa

A wani labarin, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi kira ga ‘yan Najeriya musamman manyan mutane da su yi adalci wajen sukar gwamnatinsa ta hanyar duba halin da kasar ke ciki kafin hawan gwamnatin yanzu, Daily Trust ta ruwaito.

Shugaba Buhari ya yi wannan kiran ne a ranar Alhamis a fadar gwamnati da ke Abuja, yayin da ya karbi bakuncin Reverend Yakubu Pam, Sakatare Janar na Hukumar Alhazai ta Kiristocin Najeriya.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel