2023: Manyan jiga-jigan APC sun ba Yahaya Bello da David Umahi shawarar tsayawa takaran shugaban kasa

2023: Manyan jiga-jigan APC sun ba Yahaya Bello da David Umahi shawarar tsayawa takaran shugaban kasa

- Tuni ‘yan siyasa a jam'iyyar APC suka fara tattaunawa kan 'yan takarar da ya kamata su fito a matsayin shugaban Najeriya na gaba

- Wasu shugabannin majalisa biyu a jihar Kogi da Ebonyi sun yi tallan gwamnonin su game da ragamar shugabancin

- Har yanzu APC ba ta bayyana yankin kasar da take da niyyar bai wa tikitin takarar shugabancin kasar ba

Manyan jiga-jigan jam'iyyar All Progressives Congress (APC) sun shawarci Gwamna Yahaya Bello da Gwamna David Umahi a matsayin mafi kyawun 'yan siyasa da zasu mulki Najeriya a 2023.

Shawarwarin sun fito ne daga kakakin majalisar dokokin Kogi, Mathew Kolawole, da takwaransa na majalisar Ebonyi, Francis Nwifuru.

Duk mutanen biyu a wajen taron siyasa a jihar Ebonyi sun yi ikirarin cewa Bello da Umahi suna da kwarewar da ake bukata don shugabancin kasar.

KU KARANTA: 'Yan bindiga sun kashe mutum 8, sun kone gidaje a Zamfara

2023: Manyan jiga-jigan APC sun ba Yahaya Bello da David Umahi shawarar tsayawa takaran shugaban kasa
2023: Manyan jiga-jigan APC sun ba Yahaya Bello da David Umahi shawarar tsayawa takaran shugaban kasa Hoto: @LugardHouse, @EbonyiGov
Asali: Twitter

Kamar yadda shafin jaridar The Punch ya ruwaito, kakakin majalisar jihar Kogi ya yi kira da a raba shugaban kasa zuwa yankin arewa ta tsakiya da kuma kudu maso gabas.

Kolawole ya bayyana cewa dukkanin yankunan biyu sun kasance wadanda aka fi maida hankali akansu tun bayan dawowar mulkin dimokiradiyya a shekarar 1999.

Ya ce Nijeriya za ta ci gajiyar hakan sosai tare da Bello a matsayin shugaba da Umahi a matsayin mataimakin shugaban kasa.

A daya bangaren kuma, Francis Nwifuru wanda ke shugabantar majalisar ta Ebonyi ya roki APC da ta sanya tikitin takarar ta na shugaban kasa zuwa yankin kudu maso gabas.

A cewarsa, idan kudu maso gabas ta samu tikitin, ya kamata a goyi bayan Umahi don ya mulki kasar, yayin da Gwamna Bello na iya zama mataimakin sa.

KU KARANTA: Sojoji sun kashe 'yan bindiga 35 a Zamfara da Katsina

A wani labarin, Ba da daɗewa ba za a ƙaddamar da wata jam'iyya mai ban tsoro, in ji tsohon Gwamnan Jihar Imo, Rochas Okorocha, a ranar Litinin, The Nation ta ruwaito.

Ya ce sabuwar jam'iyyar za ta samar da wani abin dogaro na gaskiya ga jam'iyyar PDP da jam'iyyar APC mai mulki.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel