An yi garkuwa da wani hakimi a Adamawa

An yi garkuwa da wani hakimi a Adamawa

- 'Yan bindiga a jihar Adamawa sun afkawa gidan wani hakimi kuma suka sace shi

- Harin ya biyo bayan alwashin da kwamishinan 'yan sandan jihar yayi

- 'Yan sanda tuni sun baza jami'ansu don gano inda yake da kuma cafke maharan

An sace wani Hakimi a jihar Adamawa a daren Litinin din da ta gabata bayan sabon Kwamishinan 'yan sanda ya sha alwashin rage aikata laifuka a gidan labarai.

Sabon kwamishinan ‘yan sanda, Aliyu Adamu, ya kira wani taron manema labarai da misalin karfe 11 na safiyar Litinin a hedikwatar‘ yan sanda ta jihar da ke Jimeta, Yola.

Yayin da ‘yan bindigar suka dauke hakimin Mayo-Farang a karamar hukumar Mayo-Belwa, Mustapha Ahmadu, a kewayen tsakar dare na wannan rana, The Nation ta ruwaito.

KU KARANTA: Wasu masu bincike a UNILORIN sun ba da shawarar amfani da abarba don magance COVID-19

An yi garkuwa da wani hakimi Adamawa
An yi garkuwa da wani hakimi Adamawa Hoto: Global Underwriters
Asali: UGC

Bayanai sun ce an sace Hakimin, wanda yake ke matsayin Sarkin Noman Adamawa, 'yan sa'o'i kadan bayan ya dawo jihar daga Abuja.

A cewar bayanan, ‘yan bindigar sun far wa fadar ne da tsakar daren ranar Litinin inda suka yi awon gaba da shi bayan sun rinjayi masu gadin fadar.

“Duka garin ya kasance cikin tashin hankali yayin da harbe-harben bindiga ke hayar iska da tsakar dare. An sace hakimin duk da kasancewar masu gadin fadar, ”inji daya daga cikin majiyar.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda ta Jihar Adamawa (PPRO), DSP Suleiman Nguroje, ya ce rundunar ta tura jami’anta don ceton hakimin tare da cafke 'yan bindigar.

A wani labarin, 'Yan bindiga sun sake kashe mutane takwas a kauyukan Dutsin Gari da Rayau da ke karamar hukumar Maru a jihar Zamfara a wani sabon hari.

Wani shaidar gani da ido, Malam Ibro Mamman ya zanta da wakilin The Punch ya ce ‘yan fashin a kan babura sun mamaye kauyen Dutsin Gari a daren jiya da niyyar yin garkuwa da wasu mutane amma mazauna garin sun fuskance su gaba daya.

KU KARANTA: Sabuwar jam'iyyar siyasa mai karfi na nan zuwa, in ji Okorocha

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel