Jerin sunaye: Hukumar yan sandan Najeriya ta sanar da sabbin nade-nade

Jerin sunaye: Hukumar yan sandan Najeriya ta sanar da sabbin nade-nade

- Hukumar yan sandan Najeriya ta sanar da sabbin sauye sauye a tsakanin jami'anta

- Rundunar ta sauya wa wasu kwamishinonin yan sanda wuraren aiki

- Har ila yau hukumar ta nada wasu jami'ai a sabbin matsayi

Hukumar yan sandan Najeriya a ranar Laraba, 13 ga watan Janairu, ta sanar da turawa tare da sauya wa wasu jam’ai wuraren aiki zuwa hukumomin rundunar tara a kokarin yin sauyi a kasar.

Mataimakin jami’in hulda da jama’a, Aremu Sikiru Adeniran ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar, a shafin sadarwa na rundunar.

Aremu ya ce sauyin zai fara aiki a nan take, inda ya kara da cewa dole dukkan jami’an da aka yi wa sauyi su koma sabbin tashoshinsu.

Jerin sunaye: Rundunar yan sandan Najeriya ta sanar da sabbin nade-nade
Jerin sunaye: Rundunar yan sandan Najeriya ta sanar da sabbin nade-nade Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

KU KARANTA KUMA: Shugaba Buhari ya amince da nadin jakadu 95

Jerin sunaye da matsayinsu sun hada da:

1. Jihar Kebbi - CP Adeleke Adeyinka Bode, mni

2. SPU, FHQ, Abuja – CP Philip Maku

3. Jihar Sokoto – CP Ali Janga Aji

4. Armament, FHQ, Abuja - CP Ohikere S. Idris, fsi

5. CMDT Police College Ikeja -CP Daniel Sokari-Pedro, mni

6. Port Authority Police (PAP), Western, Lagos - CP John O. Amadi, mni

7. Jihar Oyo - CP Ngozi Onadeko, fdc

8. Jihar Enugu - Mohammed Ndatsu Aliyu

9. Border Patrol, FHQ, Abuja - CP Haladu Musa Rosamson, fdc

10. Jihar Cross River - CP Sikiru Akande

11. Jihar Ebonyi - CP Aliyu Garba

KU KARANTA KUMA: Dan kasuwa ya sayi wayoyin iPhone har na N45m amma babu komai a kwalayen

12. Hukumar filin jirgin sama - CP Abubakar Umar Bature

13. Sashin ayyuka, FHQ - CP Yusuf Ahmed

14. Jihar Adamawa - CP Aliyu Adamu Alhaji

15. Sashin horo - CP Babaita Ishola

16. Jihar Imo - CP Nasiru Mohammed

18. Jihar Delta -CP Ari Mohammed Ali

19. Sashin yaki da ta’addanci, FHQ, Abuja - CP Olofu Tony Adejoh

20. Peacekeeping, FHQ, Abuja - CP Sadiq Idris Abubakar

21. Jami’in hulda da jama’a na rundunar - CP Frank Mba.

A wani labarin, Gamayyar kungiyoyi uku na ma'aikatan jami'a sun shirya tafiya yajin aiki idan aka gaza cimma bukatun su kafin kwana uku.

Tuni sun tsunduma zanga zanga bisa rashin amincewa da ingancin tsarin IPPIS.

Shugaban kungiyar ya ce suna da yakinin gwamnati zata duba bukatar su saboda kar su kawo tsaiko a karatun yara.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel