PDP ta shiga matsala yayinda mambobinta 2,000 suka sauya sheka zuwa APC

PDP ta shiga matsala yayinda mambobinta 2,000 suka sauya sheka zuwa APC

- Jam’iyyar APC a jihar Abia ta kara karfi yayinda ta tarbi sabbin masu sauya sheka daga PDP

- Akalla mutane 2,000 ne suka sauya sheka daga jam’iyyar adawar zuwa jam’iyya mai mulki a karamar hukumar Abia ta arewa

- Tsohon gwamnan jihar, Orji Kalu ne ya tarbi sabbin mambobin jam’iyyar a ranar Alhamis, 7 ga watan Janairu

Guguwar sauyin sheka ta sake kai wa jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ziyara yayinda mambobinta su 2,000 a karamar hukumar Abia ta arewa suka koma jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a ranar Alhamis, 7 ga watan Janairu.

A bisa wani rahoto daga jaridar The Punch, sabbin masu sauya shekar sun samu tarba a Igbere daga bulaliyar majalisar dattawa, Orji Kalu a madadin shugaban jam’iyyar, Cif Donatus Nwankpa da shugaban rikon kwarya na APC, Gwamna Mai Mala Buni.

KU KARANTA KUMA: Kyawawan masoya yan Nigeria sun raya sunnah, mutane da dama sun sanya masu albarka

PDP ta shiga matsala yayinda mambobinta 2,000 suka sauya sheka zuwa APC
PDP ta shiga matsala yayinda mambobinta 2,000 suka sauya sheka zuwa APC Hoto: @OfficialPDPNig
Asali: Twitter

Kalu yayinda yake tarban sabbin mambobin jam’iyyar, ya bukaci masu sauya shekar da su yi aiki don nasarar jam’iyyar mai mulki a zaben 2023.

Cif Mascot Kalu, dan takarar APC a zaben yan majalisar wakilai a 2019 ya yaba wa masu sauya shekar a kan hukuncin da suka yanke.

KU KARANTA KUMA: EFCC ta ce za a hukunta yan Nigeria da suka siyar da lambobinsu na NIN

A halin da ake ciki, Bunch Adiele da Eze Agege, a madadin masu sauya shekar sun ce: “Mu yayanku ne da ke zama tare da yin kasuwanci a karamar hukumar Aba ta arewa.”

A wani labarin, kotun daukaka kara na Fatakwal, jihar Ribas, ta yanke hukunci cewa Sanata Seriake Dickson yana da tambayar da zai amsa a gaban Alkali.

Babban kotun kasar ta fara yanke hukunci a shari’ar da ake yi da tsohon gwamnan na Bayelsa, inda ake neman soke takarar majalisar da ya yi.

A zaman da Alkalan kotun daukaka kara su kayi a karkashin Mai shari’a U. Onyemenam, an soki hukuncin da Alkalin babban kotun tarayya ya yi.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel