Dalilin da yasa ba zan bar PDP ba, Gwamna Ikpeazu ya magantu

Dalilin da yasa ba zan bar PDP ba, Gwamna Ikpeazu ya magantu

- Gwamna Okozie Ikpeazu ya magantu a kan rade-radin cewa yana shirin sauya sheka

- Ikpeazu ya ce sam bai ga dalilin da zai sa ya bar PDP zuwa wata jam'iyya ba

- Ya kuma jadadda cewa sune da karfi a jihar Abia

Gwamnan jihar Abia, Okozie Ikpeazu ya bayyana cewa ba zai sauya sheka daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) zuwa All Progressives Congress (APC).

Da yake watsi da rade-radin sauya shekar, ya ce batun bai da tushe saboda PDP ce jam’iyya mafi rinjaye a jihar, jaridar The Nation ta ruwaito.

Da yake magana a Umuahia, babbar birnin jihar, Ikpeazu ya ce bai ga dalilin da zai sa ya bar PDP zuwa wata jam’iyya ba.

Dalilin da yasa ba zan bar PDP ba, Gwamna Ikpeazu ya magantu
Dalilin da yasa ba zan bar PDP ba, Gwamna Ikpeazu ya magantu Hoto: BBC.com
Asali: UGC

KU KARANTA KUMA: Fastocin kamfen din Shugaban kasa na Gwamna Bello sun mamaye unguwannin Kano gabannin 2023

Ya ce: “Ban ga dalilin da zai sa na bar PDP zuwa wata jam’iyyar siyasa ba. Yadda ake murza kambun siyasa a kowani jiha ya banbanta da juna.

“A nan Abia, mutanen sun gamsu da PDP kuma ina ganin takarar Ndi Abia zai cimma nasara a karkashin inuwar jam’iyyar PDP.”

Ikpeazu ya kara da cewa: “Babu wanda ya iya gamsar dani cewa akwai wata jam’iyya a nan Abia da ta fi PDP. Ni babban dan PDP ne kuma jigo a jam’iyyar.

“Bugu da kari, ni ne mataimakin Shugaban kungiyar gwamnonin PDP. Na gwammaci na zama kwandastan mota da na zama direban motar da bata tafiya.”

KU KARANTA KUMA: Kotun daukaka kara ta fatattaki shugaban kwamitin rikon kwaryan APC a Ribas

A wani labarin, tsohon mataimakin Shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayar da bayani kan yadda jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) za ta iya yin nasara a zaben 2023.

Dan siyasan wanda yayi takarar kujerar Shugaban kasa karkashin jam’iyyar ya ce doe PDP ta hade domin samun nasara a zaben 2023, Vanguard ta ruwaito.

Ya bayar da shawarar a ranar Talata, 29 ga watan Disamba, a wani taron siyasa a karamar hukumar Afikpo ta kudu da ke yankin Ebonyi ta kudu.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel