Yanzu Yanzu: An kashe mutum 7 tare da kona gidaje a sabon harin Kaduna

Yanzu Yanzu: An kashe mutum 7 tare da kona gidaje a sabon harin Kaduna

- Wasu yan bindiga sun kai farmaki wani gari a karamar hukumar Jemaa da ke jihar Kaduna

- Maharan sun kashe mutum bakwai, sun raunata hudu sannan suka kona akalla gidaje hudu

- Harin na zuwa ne kimanin kwanaki hudu bayan yan fashi sun kashe wasu mutane hudu a Kaduna

Jihar Kaduna ta shiga juyayi bayan wani harin sassafe da aka kai sannan aka kashe akalla mutane bakwai a kauyen Ungwan Bido da ke karamar hukumar Jemaa.

Channels TV ta ruwaito cewa wasu yan bindiga da ba’a san ko su wanene ba wadanda suka far na kauyen a ranar Lahadi, 29 ga watan Nuwamba sune suka kaddamar da harin.

Har yanzu ba a ga wasu yara biyu ba bayan mummunan al’amarin yayinda maharan suka raunata mutum uku da kona gidaje hudu.

Yanzu Yanzu: An kashe mutum 7 tare da kona gidaje a sabon harin Kaduna
Yanzu Yanzu: An kashe mutum 7 tare da kona gidaje a sabon harin Kaduna Hoto: @GovKaduna
Asali: Twitter

Samuel Aruwan, kwamishinan tsaron cikin gida na jihar, wanda ya tabbatar da lamarin ya kuma bayyana cewa harin ya biyo bayan rahoton kisan wani Isiyaka Saidu.

KU KARANTA KUMA: Martanin 'yan Najeriya a kan rahoton matsawa gwamna Bello ya nemi shugaban kasa a 2023

An kashe Saidu wanda ya kasance makiyayi a kauyen Ungwan Pah a ranar Asabar, 28 ga watan Nuwamba.

A halin da ake ciki, Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna ya yi martani kan sabon harin sannan yayi Allah-wadai da lamarin.

Yayinda yake jaje ga iyalan mamatan da wadanda aka raunata, gwamnan ya umurci hukumomin tsaro da su yi bincike da kamo dukkanin masu hannu a ta’asar.

KU KARANTA KUMA: Jam’iyyar PDP na shirin tarwatsewa yayinda karin wasu gwamnoni ke barazanar komawa APC

A wani labarin kuma, Gwamna Zulum ya jagoranci jana'izar manoma 43 da Boko Haram ta yi wa yankan rago a Zabarmari da ke jihar Borno.

An tattaro cewa har yanzu ba a gama tantance adadin wadanda aka kashe ba da kuma wadanda suka bata.

A daren ranar Asabar ne dai maharan suka abka wa manoman yayin da suke girbin shinkafa kauyen Koshebe da ke karamar hukumar Mafa.

Don sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng