Yanzu Yanzu: An kashe mutum 7 tare da kona gidaje a sabon harin Kaduna

Yanzu Yanzu: An kashe mutum 7 tare da kona gidaje a sabon harin Kaduna

- Wasu yan bindiga sun kai farmaki wani gari a karamar hukumar Jemaa da ke jihar Kaduna

- Maharan sun kashe mutum bakwai, sun raunata hudu sannan suka kona akalla gidaje hudu

- Harin na zuwa ne kimanin kwanaki hudu bayan yan fashi sun kashe wasu mutane hudu a Kaduna

Jihar Kaduna ta shiga juyayi bayan wani harin sassafe da aka kai sannan aka kashe akalla mutane bakwai a kauyen Ungwan Bido da ke karamar hukumar Jemaa.

Channels TV ta ruwaito cewa wasu yan bindiga da ba’a san ko su wanene ba wadanda suka far na kauyen a ranar Lahadi, 29 ga watan Nuwamba sune suka kaddamar da harin.

Har yanzu ba a ga wasu yara biyu ba bayan mummunan al’amarin yayinda maharan suka raunata mutum uku da kona gidaje hudu.

Yanzu Yanzu: An kashe mutum 7 tare da kona gidaje a sabon harin Kaduna
Yanzu Yanzu: An kashe mutum 7 tare da kona gidaje a sabon harin Kaduna Hoto: @GovKaduna
Asali: Twitter

Samuel Aruwan, kwamishinan tsaron cikin gida na jihar, wanda ya tabbatar da lamarin ya kuma bayyana cewa harin ya biyo bayan rahoton kisan wani Isiyaka Saidu.

KU KARANTA KUMA: Martanin 'yan Najeriya a kan rahoton matsawa gwamna Bello ya nemi shugaban kasa a 2023

An kashe Saidu wanda ya kasance makiyayi a kauyen Ungwan Pah a ranar Asabar, 28 ga watan Nuwamba.

A halin da ake ciki, Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna ya yi martani kan sabon harin sannan yayi Allah-wadai da lamarin.

Yayinda yake jaje ga iyalan mamatan da wadanda aka raunata, gwamnan ya umurci hukumomin tsaro da su yi bincike da kamo dukkanin masu hannu a ta’asar.

KU KARANTA KUMA: Jam’iyyar PDP na shirin tarwatsewa yayinda karin wasu gwamnoni ke barazanar komawa APC

A wani labarin kuma, Gwamna Zulum ya jagoranci jana'izar manoma 43 da Boko Haram ta yi wa yankan rago a Zabarmari da ke jihar Borno.

An tattaro cewa har yanzu ba a gama tantance adadin wadanda aka kashe ba da kuma wadanda suka bata.

A daren ranar Asabar ne dai maharan suka abka wa manoman yayin da suke girbin shinkafa kauyen Koshebe da ke karamar hukumar Mafa.

Don sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel