Bidiyon yadda yan achaba suka fatattaki jami’an yan sanda a Lagas

Bidiyon yadda yan achaba suka fatattaki jami’an yan sanda a Lagas

- Wasu yan achaba sun fatattaki jami'an yan sanda da gudu a yankin Ikeja da ke jihar Lagas

- Lamarin ya afku ne a yau Laraba, 18 ga watan Nuwamba, inda aka gano yan sandan suna gudu ba kama hannun yaro

- Jami'an tsaron sun je yankin ne domin kama yan achaban da ke karya dokar ka'idar tuki

Jami’an yan sanda sun ci na kare a yau Laraba, 18 ga watan Nuwamba, bayan yan achaba sun fatattake su a hanyar babban titin Lagos-Abeokuta da ke yankin Ikeja, jihar Lagas.

A wani bidiyo da ya shahara, an gano wasu yan achaba suna bin jami’an tsaro da gudu, yayinda su kuma suka shige motarsu na aiki sannan suka bar wajen a guje.

An tattaro cewa jami’an tsaron sun je yankin ne domin kama baburan da suke take dokar tuki a jihar.

Bidiyon yadda yan achaba suka fatattaki jami’an yan sanda a Lagas
Bidiyon yadda yan achaba suka fatattaki jami’an yan sanda a Lagas Hoto: Lindaikejiblog
Asali: UGC

Lamarin na zuwa ne kasa da sa’o’i 24 bayan wasu masu achaba sun kara da rundunar tsaro a yankin Festac da ke jihar.

KU KARANTA KUMA: Allah ya azurta ma’auratan da suka yi shekaru 6 ba haihuwa da ‘yan uku shekaru 3 bayan sun karbi rikon wata yarinya

Ga bidiyon karawar kamar yadda shafin Lindaikejiblog ya wallafa:

KU KARANTA KUMA: Ganduje: Hukumar yaƙi da rashawa ta Kano ta fi kowacce tasiri a Nigeria

A wani labari, rundunar yan sanda a jihar Lagas a ranar Lahadi, 15 ga watan Nuwamba, ta bayyana cewa ta kama mutane 720 mabuya daban-daban a jihar duk a cikin kokarin da ake na kakkabe laifuka.

Olumuyiwa Adejobi, kakakin yan sandan jihar, a cikin wata sanarwa ya bayyana cewa rundunar ta kai samamen ne a ranar Lahadi sannan ta kama masu laifin a yankuna 14.

An kuma samo makamai, layoyi, da miyagun kwayoyi.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng