Najeriya ta kawo kudirin da zai sa a rika kai tsofaffin ‘Yan Boko Haram karatu

Najeriya ta kawo kudirin da zai sa a rika kai tsofaffin ‘Yan Boko Haram karatu

- An kawo kudirin kafa Ma’aikatar da za ta kula da tsofaffin ’Yan Boko Haram

- Majalisar dattawa ta na so a rika ba tubabbun ‘Yan ta’adda karatu mai nagarta

- Sanata Ibrahim Geidem ya kawo wannan kudiri da ya jawo ce-ce-ku-ce a kasa

Jaridar Punch ta fitar da rahoto a game da sabon kudirin da aka kawo a majalisa domin ilmantar da tsofaffin ‘yan ta’addan Boko Haram a Najeriya.

Wannan kudiri zai yi kokarin sauya tunanin tubabbun ‘Yan Boko Haram, sannan a ba su matsuguni.

Hukumomi irinsu UBEC da TETFund da gwamnatocin jihohin Arewa maso gabas ne za su kawo kudin da za ayi wa tubabbun ‘yan ta’addan hidima.

KU KARANTA: Barayi su ka kewaye Gwamnatin Buhari - Sanatan Borno

‘Yan majalisa sun kira wannan kudiri da: A Bill for the Establishment of the National Agency for the Education, Rehabilitation, De-radicalisation and Integration of Repentant Insurgents in Nigeria and for Other Connected Purposes’

A ranar Alhamis da ta gabata, aka saurari wannan kudiri a karon farko, har ya samu karbuwa. Amma kudirin na Ibrahim Geidem ya jawo surutu a waje.

Sanata Ibrahim Geidem ya bayyana dalilin kai wannan kudiri gaban majalisar dattawa, ya ce ‘yan Boko Haram da-dama su na da niyyar ajiye makamansu.

A cewar Sanatan na Yobe, wannan kudiri zai dauki dawainiyar ‘yan ta’addan da su ka ajiye kayan yaki ne, ba wadanda su ka shiga hannun jami’an tsaro ba.

KU KARANTA: ‘Yan bindiga sun dawo titin Abuja, sun yi kashe-kashe

Najeriya ta kawo kudirin da zai sa a rika kai tsofaffin ‘Yan Boko Haram karatu
Ibrahim Geidam Hoto: Nigeria-Book-of-Records
Asali: Facebook

Shugaban kasa ne zai nada shugaba da zai kula da wannan ma’aikata, wanda daga cikin aikinsa har da tura tsofaffin ‘yan ta’adda karatu a kasashen ketare.

Kudirin ya ce za a cire 0.5% daga cikin kason jihohin Arewa maso gabas, sannan hukumomin TETFund da UBEC za su ba hukumar 1% daga kasonsu.

Idan mu ka tafi yankin Neja-Delta, za mu ji cewa ‘Yan bindiga sun saki tsohon ‘Dan wwasan kwallon Najeriya, Christian Obodo da aka tsare a garin Effurun.

Tsohon Tauraron na Super Eagles, Obodo, ya fito bayan wasu 'yan sa'o'i a hannun Miyagun.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel