Delta: Christian Obodo ya fada hannun Masu garkuwa da mutane, ya fito

Delta: Christian Obodo ya fada hannun Masu garkuwa da mutane, ya fito

- Tsohon Tauraron Super Eagles, Christian Obodo, ya sake shiga hannun Miyagu

- Da ya ke akwai sauran kwana a gaba, ‘Yan bindigan sun saki wannan Mutumi

- An taba yin garkuwa da Obodo a shekarun baya har sai da aka biya wasu kudi

Tsohon ‘dan wasan kwallon kafan Najeriya, Christian Obodo, wanda aka yi garkuwa da shi a ranar Lahadi, 15 ga watan Nuwamba, 2020, ya fito.

The Nation ta fitar da rahoto cewa Christian Obodo ya samu ‘yanci a ranar Lahadi da daddare. Ba mu da labarin ko ya biya kudin fansa ko bai biya ba.

Kamar yadda rahotanni su ka zo, an sace Obodo ne a hanyar zuwa matatar mai da ke garin Effurun, da ke karamar hukumar Uvwie, a jihar Delta.

Jaridar ta tabbatar da fitowar wannan Bawan Allah daga hannun masu garkuwa da mutane dazu.

KU KARANTA: ‘Yan bindiga sun dawo titin Abuja, sun yi garkuwa da mutane

Wani abokin tsohon ‘dan kwallon, Big Sam ya shaida wa ‘yan jarida cewa: “An fito da shi. An fito da shi ne jiya. Na hadu da shi yau da safe.”

“Garin nan ya na kara zama abin tsoro. Mu na murna da ya dawo gida.” Inji Injiniya Big Sam.

Tsohon ‘dan wasan na Udinese ya fada tarkon masu garkuwa da mutanen ne yayin da ya tsaya a kan hanya domin ya saye ayaba a garin Effurun.

Ba wannan ne karon farko da aka taba sace tsohon tauraron Duniyan ba, a watan Yunin 2012, an sace shi a lokacin da ya ke hanyarsa ta zuwa coci.

KU KARANTA: 'Yan Sanda su na binciken Kocin kasar Wales, Ryan Giggs

Delta: Christian Obodo ya fada hannun Masu garkuwa da mutane, ya fito
Christian Obodo Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

Obodo mai shekara 36 a Duniya ya yi ritaya daga buga kwallo ne a kungiyar Appollon Smyrnis. Sai da aka biya kudi kafin a karbi fansarsa kwanaki.

Da aka tuntubi jami’an tsaro sun nuna ba su da masaniya game da lamarin kamar yadda kakakin ‘yan sandan Delta, Onome Onovwakpoyeya, ya fada.

A kwanakin baya kun ji cewa kwararren Kocin nan, Lionel Emmanuel Soccoia ya zama sabon mai horas da Kungiyar kwallon kafan Kano Pillars.

Gwamnatin Kano ta amince da nada Bafaranshen a matsayin Kocin kungiyar kwallon kafan.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng