Yawancin yan bindigar da ke Katsina daga Zamfara suke shigowa, in ji Gwamna Masari

Yawancin yan bindigar da ke Katsina daga Zamfara suke shigowa, in ji Gwamna Masari

- Yan bindiga na ta’asa a Katsina sannan su tsere zuwa Zamfara don buya

- Wannan shine matsayar Gwamna Bello Masari na jihar Katsina

- Masari ya kara da cewa kimanin 99% na miyagun da ke garkuwa da mutane, kisa da sata a jiharsa sun fito ne daga Zamfara

Gwamnan jihar Katsina, Bello Masari, a ranar Litinin, 16 ga watan Nuwamba, ya koka kan ayyukan yan bindiga a jiharsa.

Masari, wanda ya yi magana da manema labarai a Kafur ya bayyana cewa mafi akasarin wadannan miyagun su kan je su haddasa tashin hankali a Katsina sannan su koma mabuyarsu a Zamfara, jaridar The Nation ta ruwaito.

Gwamnan ya yi korafin cewa yan bindigan na yin duk abunda za su iya don wargaza kokarinsa na dawo da zaman lafiya, tsaro da oda a Katsina.

KU KARANTA KUMA: Covid-19: Yadda muka ciyar da iyalai 127,588 lokacin kulle - Minista Sadiya

Yawancin yan bindigar da ke Katsina daga Zamfara suke shigowa, in ji Gwamna Masari
Yawancin yan bindigar da ke Katsina daga Zamfara suke shigowa, in ji Gwamna Masari Hoto: @THISDAYLIVE
Asali: Facebook

Ya yi kira ga rundunar sojin Najeriya da taimakon sauran hukumomin tsaro da suyi abunda za su iya domin fitar da yan bindigan.

Gwamnan ya ce:

“Wuraren da muke da matsala kawai sune kananan hukumomin Faskari, Sabwa da Dandume a jihar, a yankunan Jibia, Batsari, Safana da Danmusa an samu zaman lafiya.

“Daga rahotannin, da nake samu duk safe idan ka ga lamarin fashin shanu ko garkuwa da mutane toh yawacinsu a kewayen Faskari, Sabwa da Dandume ne. Muna ta kai wa hukumar soji korafi a kan su karbe ragamar yankunan Gurbi-Gidan Jaja-Kaura Namode na jihar Zamfara.

“Har sai an dawo da cikakken tsaro a wannan yankuna, kasancewarsu masu hatsari inda yawancin yan bindiga ke zama da yawo kai tsaye, idan ba haka ba, ba za mu iya kare Katsina ba ba tare da tsaro a Zamfara ba, saboda kaso 99 na dukkanin hare-hare da garkuwa da mutane da ke faruwa a Katsina daga Zamfara ne."

KU KARANTA KUMA: Akwai dalili: Budurwa ta rataye kanta a Kano

A gefe guda, Wasu sarakunan Arewa sun nuna damuwa a kan tabarbarewar ilimin yara mata a wasu jihohin arewa guda biyar, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Sarakunan sun ce rashin tsaro, talauci, rashin ilimi da sauran kalubale, sune suke tabarbarar da ci gaban ilimin yara mata a jihohi irin Borno, Zamfara, Gombe, Sokoto da Kebbi.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel