Babban jigon APC Samuel Ojebode ya rasu a Oyo

Babban jigon APC Samuel Ojebode ya rasu a Oyo

- Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta rasa wani babban jigonta, Samuel Ojebode, a Oyo

- Ojebode, ya kasance Shugaban jam’iyyar a mazabar tarayya ta Oyo

- Wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyyar sun nuna alhininsu kan mutuwar Ojebode

Abun bakin ciki da alhini ya samu jam’iyyar All Progressives Congress (APC) yayinda ta rasa daya daga cikin manyan jiga-jiganta, Samuel Ojebode.

Ojebode, wanda ya kasance jigon APC a jihar Oyo, ya rasu a ranar Asabar, 14 ga watan Nuwamba, yana da shekaru 87 a duniya.

A wani sakon ta’aziyya, wani sanata daga jihar, Teslim Folarin, ya nuna bakin cikinsa.

KU KARANTA KUMA: Tsegumi da nishaɗi: Amaryar hadimin Buhari ta aikewa mijinta Bashir Ahmad zafafan kalamai

A wani jawabi daga Yakeeen Olaniyi a Ibadan, Folarin ya bayyana mutuwar a matsayin wani babban asara ga ahlin APC a Najeriya.

Babban jigon APC Samuel Ojebode ya rasu a Oyo
Babban jigon APC Samuel Ojebode ya rasu a Oyo Hoto: Lailanews.com
Asali: UGC

Folarin ya tuna cewa jigon na APC ya shirya taro na lumana mai cike da nasara ga mambobin jam’iyyar a mazabar Oyo ta tarayya.

Ya ce Ojebode ya kasance shugaba abun koyi, mai mutunci da kima.

A sakon ta’aziyyarsa, kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Farfesa Adeolu Akande, Shugaban hukumar NCC, ya yi ta’aziyya ga iyalai, abokai da mambobin APC a jihar kan wannan rashi.

KU KARANTA KUMA: Wata sabuwa: ‘Yan bindiga sun sace malamin kwalejin Nuhu Bamalli da yara 2 a Zariya

A cewar Akande, Ojebode ya kasance dan siyasa na hakika kuma shugaba dab a a cika samun irinsa ba sannan cewa za a yi kewarsa.

A wani labari na daban, kwamishinan lafiya na jihar Benue, Dr Emmanuel Ikwulono, ya rasu, Nigerian Tribune ta ruwaito.

A ranar 5 ga watan Agustan 2020 ne aka rantsar da Dr Ikwulono a matsayin kwamishinan lafiya da harkokin jama’a na jihar Benue.

Ya maye gurbin Dr Sunday Ongbabo wanda ya yi murabus daga majalisar zartarwa ta jihar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel