Zaben shugaban kasa: Zan sake kafa tarihi a kasar Amurka - Trump

Zaben shugaban kasa: Zan sake kafa tarihi a kasar Amurka - Trump

- A yau, Talata, uku ga watan Nuwamba ake gudanar da zaben kujerar shugaban kasa a kasar Amurka

- Amurkawa na da zabin kada kuri'a ga daya daga cikin 'yan takara guda biyu; Donald Trump da Sanata Joe Biden

- Trump ya na takara ne a karkashin inuwar jam'iyyar 'Republican' yayin da Biden ke takara a karkashin inuwar jam'iyyar 'Democrat'

Shugaban ƙasa Donald Trump ya jaddada cewa zai sake kafa tarihi a yayin da Amurkawa ke jefa ƙuri'un su a ranar Talata.

A ranar Litinin ne Trump ya kammala rufe yaƙin nenan zaɓensa a cikin ɗumbin cikowar jama'a a jihohi huɗu na Amurka.

Trump ya nanata maganar aringizon ƙuri'u da aka yi masa.

Da yake jawabi a gaban jama'ar da safiyar ranar Talata a Grand Rapids,Michigan,in zaku tuna nan ne wurin da Trump ya kammala yaƙin neman zaɓen sa a shekarar 2016.

KARANTA: Najeriya ta ƙara faɗawa tsilla-tsilla sakamakon faɗuwar farashin ɗanyen man fetur

Trump mai shekaru 74 ɗan takarar jam'iyyar Republican ya ce zai sake komawa a karo na biyu.

Zaben shugaban kasa: Zan sake kafa tarihi a kasar Amurka - Trump
Zaben shugaban kasa: Zan sake kafa tarihi a kasar Amurka - Trump @TheNation
Asali: Twitter

"Zamu sake samun kyakkyawar nasara a wannan zaben," Trump ya gayawa taron jama'ar Michigan, wadanda suka yi ihu tare da hada bakin wajen yi masa jinjinar "muna sonka, muna sonka"

"Zamu sake kafa tarihi a wani karon" a Trump.

KARANTA: 2020: Yadda za a duba sakamakon jarrabar WAEC cikin sauki ta hanyar bin matakai 7

A ranar Asabar, 31 ga watan Okotoba, ne Legit.nga Hausa ta wallafa rahoton cewa an soke al-amurran yaƙin neman zaɓen Sanata Joe Biden ɗan takarar shugaban ƙasar Amurka a inuwar jam'iyyar Democrat sakamakon barazana daga magoya bayan shugaba Donald Trump.

Ƴan jam'iyyar Democrat sun ce an soke gangamin yaƙin neman zaɓen ne wanda aka shirya yinsa ranar juma'a a Pflugerville, wani gari a Texas, saboda dalilai na tsaro da shawarwari makamantan hakan.

Acewarsu, motar yaƙin neman zaɓen Biden/Harris ta tsaya cak a kan hanya sakamakon tsinke da gungun magoya bayan Trump suka yi mata.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel