Zaben shugaban kasa: Zan sake kafa tarihi a kasar Amurka - Trump

Zaben shugaban kasa: Zan sake kafa tarihi a kasar Amurka - Trump

- A yau, Talata, uku ga watan Nuwamba ake gudanar da zaben kujerar shugaban kasa a kasar Amurka

- Amurkawa na da zabin kada kuri'a ga daya daga cikin 'yan takara guda biyu; Donald Trump da Sanata Joe Biden

- Trump ya na takara ne a karkashin inuwar jam'iyyar 'Republican' yayin da Biden ke takara a karkashin inuwar jam'iyyar 'Democrat'

Shugaban ƙasa Donald Trump ya jaddada cewa zai sake kafa tarihi a yayin da Amurkawa ke jefa ƙuri'un su a ranar Talata.

A ranar Litinin ne Trump ya kammala rufe yaƙin nenan zaɓensa a cikin ɗumbin cikowar jama'a a jihohi huɗu na Amurka.

Trump ya nanata maganar aringizon ƙuri'u da aka yi masa.

Da yake jawabi a gaban jama'ar da safiyar ranar Talata a Grand Rapids,Michigan,in zaku tuna nan ne wurin da Trump ya kammala yaƙin neman zaɓen sa a shekarar 2016.

KARANTA: Najeriya ta ƙara faɗawa tsilla-tsilla sakamakon faɗuwar farashin ɗanyen man fetur

Trump mai shekaru 74 ɗan takarar jam'iyyar Republican ya ce zai sake komawa a karo na biyu.

Zaben shugaban kasa: Zan sake kafa tarihi a kasar Amurka - Trump
Zaben shugaban kasa: Zan sake kafa tarihi a kasar Amurka - Trump @TheNation
Asali: Twitter

"Zamu sake samun kyakkyawar nasara a wannan zaben," Trump ya gayawa taron jama'ar Michigan, wadanda suka yi ihu tare da hada bakin wajen yi masa jinjinar "muna sonka, muna sonka"

"Zamu sake kafa tarihi a wani karon" a Trump.

KARANTA: 2020: Yadda za a duba sakamakon jarrabar WAEC cikin sauki ta hanyar bin matakai 7

A ranar Asabar, 31 ga watan Okotoba, ne Legit.nga Hausa ta wallafa rahoton cewa an soke al-amurran yaƙin neman zaɓen Sanata Joe Biden ɗan takarar shugaban ƙasar Amurka a inuwar jam'iyyar Democrat sakamakon barazana daga magoya bayan shugaba Donald Trump.

Ƴan jam'iyyar Democrat sun ce an soke gangamin yaƙin neman zaɓen ne wanda aka shirya yinsa ranar juma'a a Pflugerville, wani gari a Texas, saboda dalilai na tsaro da shawarwari makamantan hakan.

Acewarsu, motar yaƙin neman zaɓen Biden/Harris ta tsaya cak a kan hanya sakamakon tsinke da gungun magoya bayan Trump suka yi mata.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng