Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 1 a yau a Abuja

Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 1 a yau a Abuja

Labarin da ke shigowa da daga cibiyar takaita yaduwar cuttutuka a Najeriya NCDC ta bayyana cewa an samu karin mutum daya da ya kamu da cutar Coronavirus a birnin tarayya, Abuja.

Mun kawo muku cewa A yau Lahadi, gwamnatin tarayya ta sanar da cewa na samu karin mutane hudu masu dauke cutar coronavirus (COVID-19), yanzu adadin masu cutar a Najeriya 26.

Hukumar takaita yaduwar cututtuka (NCDC) ta sanar da hakan da safiya Lahadi a shafin raayi da sada zumuntarta na Tuwita.

Jawabin yace “Misalin karfe 08:05 am na ranar 22 ga Maris, an tabbatar da asu dauke da cutar Coronavirus 26 a Najerita. Cikinsu an sallami biyu da suka samu sauki.“

“Don sanin adadin wadanda suka kamu da cutar, ku garzaya http://covid19.ncdc.gov.ng“

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng