Yanzu Yanzu: Kungiyar gwamnonin arewa sun zabi shugaba, za su kafa wata kwamitin hadin gwiwa

Yanzu Yanzu: Kungiyar gwamnonin arewa sun zabi shugaba, za su kafa wata kwamitin hadin gwiwa

- Kungiyar gwamnonin arewa sun yi zaben sabon shugabansu a yau Juma'a, 17 ga watan Mayu

- Gwamnan jihar Plateau, Simon Lalong ne yayi nasarar hayewa wannan kujera bayan ya samu goyon baayan takwarorinsa

- An gudanar da zaben sabon shugaban ne a jihar Kaduna, a taron farko da kungiyar tayi a wannan shekarar

- Gwamnonin sun kuma yanke shawarar ganawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari kan matsalolin tsaro a yankin

Gwamnan jihar Plateau, Simon Lalong ya zama shugaban kungiyar gwamnonin arewa na wasu shekaru hudu masu zuwa.

Takwarorinsa ne suka zabe shi a lokacin taron kungiyar gwamnonin arewa wanda ya gudana a Kaduna a ranar Juma’a, 17 ga watan Mayu.

A wajen taron wanda shine na farko a shekarar nan, gwamnonin sun amince da kafa wani hukumar kudi na hadin gwiwa wanda zai taimaka wajen kawo ci gaban al’umma da tattalin arziki a yankin sannan hakan zai bayar da damar dogaro da kai ta bangaren kudi.

Yanzu Yanzu: Kungiyar gwamnonin arewa sun zabi shugaba, za su kafa wata kwamitin hadin gwiwa
Yanzu Yanzu: Kungiyar gwamnonin arewa sun zabi shugaba, za su kafa wata kwamitin hadin gwiwa
Asali: Facebook

Gwamnonin sun kuma yanke shawarar ganawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari kan matsalolin tsaro a yankin.

KU KARANTA KUMA: Lalong ya kwaikwayi Ganduje, ya kasafta masarautar Jos

Ana sanya ran ganawar gwamnonin wanda daga bisani ya shiga sirri, zai samu jawabai akan yanayin tsaro a fadin jihohin da kuma sadaukarwa daga jami’an kamfanin ci gaban arewacin Najeriya kan nasarorin da aka samu a fannin hako mai a tafkin Chadi, da kuma farfado da durkusashen kamfanin buga kayayyaki na Kaduna mallakar jihohin arewa 19.

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Ga masu bukatar manhajar mu na Azumi a wannan wata mai albarka sai a bibiyi wannan shafi https://fb.gg/play/ramadan_ramadan

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng