Jirgin yaki ya lalata sansanin horar da yan Boko Haram a Malkonory, Borno

Jirgin yaki ya lalata sansanin horar da yan Boko Haram a Malkonory, Borno

- Jirgin yaki na sojin saman Najeriya ya lalata wani sansanin horar da ýan Boko Haram a Malkonory

- Hakazalika sun lalata mutor yan ta’addan a kusa Tumbun Rego a yankin arewacin Borno

- Lamarin ya afku ne a ranar Alhamis, 11 ga watan Oktoba

Rundunar sojin saman Najeriya tace jirginta na Operation Lafiya Dole ta lalata wani sansanin horar da ýan Boko Haram a Malkonory, sannan kuma sun lalata mutor yan ta’addan a kusa Tumbun Rego a yankin arewacin Borno.

Air Commodore Ibikunle Daramola, jami’in hulda da jama’a na rundunar sojin saman wanda ya bayyana hakan a wani jawabi a Abuja a ranar Alhamis, yace an gudanar da aikin ne a ranar 11 ga watan Oktoba.

Jirgin yaki ya lalata sansanin horar da yan Boko Haram a Malkonory, Borno
Jirgin yaki ya lalata sansanin horar da yan Boko Haram a Malkonory, Borno
Asali: Twitter

Daramola ya bayyana cewa sashin kwararru na NAF wato Intelligence, Surveillance and Reconnaissance (ISR) sun tabbatar da cewa a sansanin akwai maza da dama da ake horarwa.

KU KARANTA KUMA: 2019: Wata kungiya ta bukaci Atiku da ya zabi Fayose a matsayin abokin takara

Kakakin NAF din ya kuma bayyana cewa an halaka sauran tsirarun yan ta’addan a hare-haren da suka biyo baya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewar ku tare da mu.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng