AFCON 2025: Morocco Ta Gamu da Babbar Matsala Tana Shirin Karawa da Najeriya

AFCON 2025: Morocco Ta Gamu da Babbar Matsala Tana Shirin Karawa da Najeriya

  • Kocin Morocco Walid Regragui ya tabbatar da cewa dan wasa Azzedine Ounahi ba zai buga wasan Najeriya ba saboda raunin da samu
  • Super Eagles zata rasa Wilfred Ndidi sakamakon katin gargadi biyu yayin da kocin Luc Eymael ke hasashen Morocco za ta lallasa Najeriya
  • Najeriya da Morocco za su fafata a daren yau a birnin Rabat domin neman gurbin shiga wasan karshe na gasar AFCON ta shekarar 2025

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Morocco - Kocin tawagar Atlas Lions ta Morocco, Walid Regragui, ya tabbatar da cewa za su rasa babban ɗan wasan tsakiyarsu, Azzedine Ounahi, a wasansu da Najeriya

Walid Regragui ya ce Ounahi ba zai samu damar buga wasan kusa da na ƙarshe na gasar AFCON 2025 da za su fafata da Super Eagles ta Najeriya a yau Laraba, 14 ga Janairu, 2026.

Kara karanta wannan

AFCON 2025: An fadawa Najeriya abin da za ta yi don doke Morocco a 'semi finals'

Morocco ta rasa babban dan tsakiyarta, Azzedine Ounahi gabanin wasa da Najeriya.
'Yan wasan Morocco, ciki har da Brahim Diaz suna murnar cin kwallo a AFCON 2025. Hoto: Abdel Majid Bziquat
Source: Getty Images

Morocco ta samu matsala gabanin wasa da Najeriya

Wannan sanarwa ta zo ne a matsayin babban kalubale ga kasar mai masaukin baki, duba da irin muhimmancin da dan wasan yake da shi a tsarin wasan Regragui, in ji rahoton Own Goal Nigeria.

Ounahi, ɗan shekara 25, bai riga ya warke daga raunin da ya sanya ya rasa wasannin zagaye na 16 da na kusa da na kusa da na ƙarshe ba.

Rabon sa da buga wasa tun nasarar da suka samu a kan Zambia da ci 3-0 a matakin rukuni, inda ya taimaka aka zura ƙwallaye biyu.

Ko da yake Regragui ya yi wa manema labarai wasan barkwanci da farko cewa ɗan wasan ya dawo, daga baya ya tabbatar da cewa:

“Ina maku wasa ne, Ounahi ba zai buga wasan ba saboda rauni. Sai dai Kyaftin Romain Saïss ya warke kuma zai iya taka leda.”

Kara karanta wannan

AFCON 2025: Abin da muka sani game da Laryea, alkalin wasan Najeriya da Morocco

Nakasu ga Najeriya a karawa da Morocco

A hannu guda, Najeriya ma za ta fuskanci nakasu a tsakiyar fili, domin Kyaftin Wilfred Ndidi ba zai buga wasan ba saboda dakatarwa bayan ya samu katin gargadi biyu a wasannin baya.

Legit Hausa ta rahoto cewa wannan zai tilasta wa kocin Super Eagles neman wanda zai maye gurbin Ndidi domin fuskantar barazanar Morocco a filin wasa na Prince Moulay Abdellah da ke Rabat.

Tsohon kocin Chippa United, Luc Eymael, ya yi hasashen cewa Morocco ce za ta yi nasara a kan Najeriya, in ji rahoton Flash Score.

Najeriya da Morocco za su buga wasan kusa da na karshe na gasar AFCON a ranar Laraba, 14 ga Janairu, 2025.
Victor Osimhen da Brahim Diaz a hoton da ke nuna karawa Najeriya da Morocco a AFCON 2025, semi finals. Hoto: @caf_online
Source: Instagram

'Morocco ce za ta ci wasan' - Eymael

Eymael ya bayyana cewa Morocco tana buga ƙwallo a tsari mai kyau kuma za ta samu tarin magoya baya da suka kai 70,000 a filin wasanta na gida.

Ya tunatar da cewa Najeriya na da tarihin rashin nasara kwanan nan, ciki har da rasa gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026 a hannun DR Congo.

Kara karanta wannan

AFCON 2025: Bature ya hango kasar da za ta yi nasara a wasan Najeriya da Morocco

A cewarsa, ko da yake duka ƙasashen biyu za su ci ƙwallo, amma Morocco ce za ta kai wasan ƙarshe na AFCON 2025.

Wannan fafatawa ta yau 14 ga Janairu, 2026, ita ce ta shida tsakanin ƙasashen biyu a tarihin AFCON, kuma ita ce ta farko cikin shekaru 22.

'Najeriya za ta lallasa Morocco' - Bature

A wani labarin na daban, Legit Hausa ta rahoto cewa wani bature ya yi hasashen cewa Najeriya ce za ta lallasa Morocco a wasan kusa da na karshe na gasar AFCON 2025.

Baturen wanda ya yi amfani da kwan roba wajen samar da hasashensa, ya nuna cewa Morocco za ta sha kashi a hannun Super Eagles, ko da kuwa za ta zura kwallaye.

Masu sharhi sun yi gargadin cewa rashin nasarar Najeriya na iya haifar da zargin nuna son kai ga kasar Morocco dake masaukin bakin gasar.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com