AFCON 2025: Bature Ya Hango Kasar da Za Ta Yi Nasara a Wasan Najeriya da Morocco

AFCON 2025: Bature Ya Hango Kasar da Za Ta Yi Nasara a Wasan Najeriya da Morocco

  • Wani bature ya janyo ce-ce-ku-ce bayan ya yi amfani da ƙwai wajen hasashen cewa Najeriya zata doke Morocco a gasar AFCON 2025
  • Ma'abota yanar gizo sun bayyana ra'ayoyi daban-daban inda wasu suka ce Najeriya zata samu nasara idan aka yi adalci a wasan na gobe
  • Masu sharhi sun yi gargadin cewa rashin nasarar Najeriya na iya haifar da zargin nuna son kai ga kasar Morocco dake masaukin bakin gasar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta ya nuna yadda wani Bature ya yi hasashen yadda za ta kaya a wasan kusa da na karshe na gasar AFCON a gobe Laraba.

Baturen ya yi amfani da ƙwai guda biyu (wadanda ya sanya wa launukan koraye da ja) domin yin hasashen sakamakon wasan tsakanin Najeriya da Morocco.

Kara karanta wannan

Bashir Ahmad ya soki Abba Kabir kan tsawaita maganar zuwa APC, ya fadi illar dambarwar

Bature ya hango nasarar Najeriya a wasanta da Morocco a AFCON 2025
Tawagar Morocco da tawagar Najeriya da za su fafata a gasar AFCON 2025 ranar Laraba. Hoto: @lionsdelatlass, @NGSuperEagles
Source: Twitter

Hasashen wasan Najeriya da Morocco

A cikin bidiyon da ya wallafa a shafinsa ta TikTok, mutumin ya zubar da ƙwan guda biyu lokaci ɗaya domin ganin wanda zai yi nasara.

An ga yadda jar kwallo, wacce ke alamta Morocco ta shiga rami sau uku, kafin koriyar kwallo, wacce ke alamta Najeriya ta zo ta shiga ramin har sau hudu, wanda ya nuna Najeriya ce za ta ci wasan.

Wannan hasashen ya janyo ce-ce-ku-ce daga ’yan Najeriya a ƙarƙashin bidiyon, inda wasu suka yi masa gargaɗin cewa ya gode wa Allah da ya nuna Najeriya ce za ta ci, idan ba haka ba da ya fuskanci fushin dubban masu amfani da yanar gizo.

Wasu kuwa sun yi imanin cewa wannan wasa da za a yi ranar Laraba, 14 ga Janairu, 2026, zai kasance mai zafi sosai duba da yadda Morocco ce mai masaukin baƙi.

Nasarar Najeriya da Moroko a wasannin baya

Kara karanta wannan

Kano da wasu jihohin Najeriya 4 da siyasarsu ke ɗaukar zafi gabanin zaɓen 2027

Wasan kusa da na ƙarshen tsakanin Super Eagles da Atlas Lions zai gudana ne a babban filin wasa na Prince Moulay Abdellah da ke birnin Rabat.

Najeriya ta isa wannan mataki ne bayan ta doke Algeria da ci 2-0 a wasan daf da na kusa da na ƙarshe, inda Victor Osimhen da Akor Adams suka zura ƙwallayen, in ji rahoton Legit Hausa.

A hannu guda kuma, Morocco ta doke Kamaru ne da ci 2-0 don tabbatar da matsayinta, tare da shiga zagayen kusa da na karshe, a cewar rahoton BBC.

Wani matashi ya ce Najeriya za ta yi korafi mai yawa idan ba ta yi nasara kan Morocco a gasar AFCON 2025 ba.
'Yan wasan Najeriya, watau Super Eagles sun yi sahu a filin wasa. Hoto: @NGSuperEagles
Source: Getty Images

Abin da zai faru idan Najeriya ta sha kasa

Wani matashi ɗan Najeriya mai suna Menjo shi ma ya bayyana ra'ayinsa kan wasan, inda ya gargaɗi hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka (CAF) da alkalan wasa.

A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Menjo ya ce:

  • Idan Najeriya ta doke Morocco, komai zai tafi lafiya lau.
  • Amma, idan Morocco ta doke Najeriya, "to lamura za su cukurkude."

Ya bayyana cewa idan Najeriya ta sha kashi, ’yan ƙasar za su zargi CAF da nuna son kai ga Morocco a matsayinta na mai masaukin baki, ko kuma zargin alƙalin wasa da rashin adalci wajen bayar da fanareti ko soke ƙwallaye.

Kara karanta wannan

AFCON 2025: Osimhen ya fadi yadda Super Eagles ke kallon wasa da Morocco

Najeriya na neman kofinta na hudu ne, yayin da Morocco ke son kafa tarihi a gida tun bayan nasarar su ta karshe a 1976.

Ra'ayin wasu 'yan Najeriya

Legit Hausa ta ji ra'ayoyin wasu masu kallon kwallo game da hasashen wannan bature:

Mukhtasir Hamza:

"Hasashensa yana kan hanya, haka muke fatan Allah ya ba mu sa a a wasan nan."

Hamza Hamza:

"Ai dama kowa ma ya san Najeriya ce ta fi karfin daukar kofin nan, sai dai mutum ya ki gaskiya. Muna yi wa Osimhen, Lookman da sauran 'yan wasanmu fatan alheri. Up Super Eagles!"

Fahad Hamza:

"Ni nan har wata kwarya kwaryar walima na shirya, idan Najeriya ta doke Morocco to lallai za mu yi walima da kaji, idan kuma ta daga kofi, to za mu yanka ko rago ne, wannan alkawari ne. In Sha Allahu mu ne da nasara."

BUA ya gwangwaje 'yan wasan Najeriya

A wani labari, mun ruwaito cewa, Abdulsamad Rabiu ya taya Super Eagles murnar doke Algeria, tare da alkawarin ba ’yan wasan kyautar N700,000.

Kara karanta wannan

AFCON2025: Mourinho ya hango kasar da za ta yi nasara a wasan Najeriya da Moroko

Abdussamad Rabiu ya ce zai ƙara ba da $50,000 kan kowace kwallo da aka ci a wasan kusa da na ƙarshe da Najeriya za ta buga a gasar bana.

Attajirin Najeriyar ya kuma yi alkawarin $1,000,000 idan Super Eagles ta lashe wasan ƙarshe, tare da ƙarin $100,000 ga kowace kwallo da aka ci a Morocco.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com