Albashin ma'aikatan najeriya
Gwamna Okpebholo ya ƙara mafi karancin albashi zuwa ₦75,000 ga ma’aikatan Edo tare da ɗaukar sababbin malamai da ma’aikatan lafiya a fadin jihar.
Hukumar FGSHLB ta fara tattara jerin sunayen ma'aikatan da suka yi ritaya da suka kasa biyan cikakken lamunin gidajen da suka samu daga gwamnatin tarayya.
Hukumar tattara kudin shiga da raba su, RMAFC, ta yi karin haske kan albashin shugabanni inda ta ce bai da yawa kamar yadda ake tunani kuma bai karu tun 2007 ba.
Ma’aikatan NiMet sun fara yajin aiki a dukkanin fadin Najeriya. Ma'aikatan sun yi korafi na karancin albashi da yanayin aiki mai kyau. Sun nemi a dauki mataki.
Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya tuna da ma'aikatan da suka yi ritaya da wadanda suka rasu. Gwamnan ya umarci a fitar da kudade domin biyansu hakkokinsu.
Shugaban rikon kwarya a jihar Rivers, Vice Admiral, Ibok-Ete Ibas ya umarci a biya ma’aikatan kananan hukumomi albashin da suke bi ba tare da bata lokaci ba.
Shugaban hukumar kula da masu yi wa kasa hidima (NYSC), Birgediya-Janar Olakunle Oluseye Nafiu, ya ba da tabbaci kan lokacin fara biyan alawus na N77,000.
Kungiyar kwadago ta kasa (NLC) ta bayyana irin kokarin da ta yi wajen samo wa ma'aikatan ƙasar nan mafi karancin albashi mai tsoka, amma ta ce ta fuskanci kalubale.
'Yan majalisa sun ba Tinubu gudunmawar N705m domin a ragewa talakawa radadin wahalar tattalin arziki, sun ce sun cika alkawarin ba da rabin albashinsu ga mabukata.
Albashin ma'aikatan najeriya
Samu kari