Albashin ma'aikatan najeriya
Ma’aikatan NiMet sun fara yajin aiki a dukkanin fadin Najeriya. Ma'aikatan sun yi korafi na karancin albashi da yanayin aiki mai kyau. Sun nemi a dauki mataki.
Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya tuna da ma'aikatan da suka yi ritaya da wadanda suka rasu. Gwamnan ya umarci a fitar da kudade domin biyansu hakkokinsu.
Shugaban rikon kwarya a jihar Rivers, Vice Admiral, Ibok-Ete Ibas ya umarci a biya ma’aikatan kananan hukumomi albashin da suke bi ba tare da bata lokaci ba.
Shugaban hukumar kula da masu yi wa kasa hidima (NYSC), Birgediya-Janar Olakunle Oluseye Nafiu, ya ba da tabbaci kan lokacin fara biyan alawus na N77,000.
Kungiyar kwadago ta kasa (NLC) ta bayyana irin kokarin da ta yi wajen samo wa ma'aikatan ƙasar nan mafi karancin albashi mai tsoka, amma ta ce ta fuskanci kalubale.
'Yan majalisa sun ba Tinubu gudunmawar N705m domin a ragewa talakawa radadin wahalar tattalin arziki, sun ce sun cika alkawarin ba da rabin albashinsu ga mabukata.
Gwamnatin Kano ta bukaci ma’aikatan jihar da su tantance albashinsu na Maris, kafin ta fara biya, tana mai cewa za a biya kafin Sallah don su samu walwala.
Ma'aikatun gwamnatin Bola Ahmed Tinubu guda biyu sun bayyana shirin hadin gwiwa da zai bayar da damar samawa 'yan kasar nan ayyuka akalla miliyan biyar.
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya dakatar da mukaddashin shugaban ma'aikatan jihar, Salisu Mustapha kan zargin cire kudi daga albashin ma'aikata ba bisa ka’ida ba.
Albashin ma'aikatan najeriya
Samu kari