Labaran tattalin arzikin Najeriya
Gwamnatin tarayya ta nada kwamishinonin haraji da za su warware rikici da tabbatar da ba wanda ya kaucewa biyan haraji a Najeriya. Wale Edun ne ya tabbatar da haka.
Gwamnatin Katsina ta ware Naira biliyan 2.3 domin samar da abinci domin ciyar da talakawa a watan Ramadan. Shirin na cikin kokarin gwamna Radda ga talakawa.
Gwamnatin Tarayya ta raba dala miliyan 68.36 ga jihohi 28 a ƙarƙashin shirin SABER don inganta kasuwanci, sauƙaƙa dokoki, da jawo zuba jari a Najeriya.
Gwamnatin tarayya ta bukaci ‘yan kasuwa su rage farashin kayan abinci yayin da ta tallafa wa manoman Jigawa da kayayyakin noma na Naira biliyan 5.
Mai kudin Afrika, Aliko Dangote ya bayyana kalubalen da ya fuskanta yayin gina matatar mai da ke Legas. Ya ce da ya gaza karasa aikin da ya samu karayar arziki.
Hukumar kididdiga ta kasa watau NBS ta bayyana cewa hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya ya yi gagarumar faɗuwa daga 34% zuwa 24.48% a watan Janairu.
Karamin Ministan tsaro, kuma tsohon gwamnan Zamfara, Bello Matawalle ya bayyana cewa 'yan Arewa su na ganin amfanin mulkin Bola Ahmed Tinubu a fannoni da dama.
Gwamnatin tarayya ta nemi sabon bashin dala miliyan 300 daga Bankin Duniya don inganta kiwon lafiya, NCDC ce za ta aiwatar da shirin a shekarar 2026.
Daya daga cikin sababbin limaman masallacin Abuja, Abdulkadir Salman Sholagberu ya bukaci yan Najeriya su koma ga Ubangiji kan tsadar rayuwa da ake ciki.
Labaran tattalin arzikin Najeriya
Samu kari