Musulmai
Wasu majiyoyi sun tabbatar da mana da cewa ‘yan sandan Osun ta kama wani malamin addini da ake zargi da lalata wata yarinya ‘yar shekara takwas a Ede.
Malamin addinin Musulunci a Najeriya ya yi bayani kan hukuncin kai gawa daga wani gari zuwa kasa mai tsarki kamar Madina a birne ta bayan jana'izar Aminu Dantata.
Bayan kwanaki da rasuwarsa, an yi jana'izar fitaccen ɗan kasuwar nan, Alhaji Aminu Ɗantata a birnin Madina, manyan mutane daga ciki da wajen Najeriya sun halarta.
Rahotanni sun nuna cewa an matsar da jana'izar marigayi Alhaji Aminu Ɗantata daga lokacin sallar la'asar zuwa bayan Magriba a masallacin Annabi SAW da ke Madina.
Rahotanni sun bayyana cewa an tura malamar addinin Musulunci daga Ibadan, Alhaja Kafilat Kaola gidan gyaran hali na Oke Kura a Ilorin a jihar Kwara.
Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III ya bukaci a cigaba da addu'a a kan rashin tsaron Najeriya. Ya yi magana kan yakin Iran da Isra'ila.
Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda ya ayyana ranar huti domin murnar shigowar sabuwar shekarar musulunci ta 1447 bayan Hijira. Ya bukaci a yi addu'o'i.
A labarin nan, za a ji cewa wasu daga cikin jihohi ƙasar nan sun ayyana ranar 1 ga watan Muharram a matsayin hutu ga ma'aikata saboda shigowar shekarar musulunci.
Kasar Saudiyya da sarkin Musulmi sun sanar da shiga sabuwar shekarar Musulunci ta 1447 a ranar Alhamis. Za a yi azumin ashura a ranar 10 ga wata.
Musulmai
Samu kari