Karatun Ilimi
Gwamna Seyi Makinde ya amince da ɗaukar malaman makaranta 7,000 da ma'aikata 100 a makarantun naƙasassu domin ingantar harkar neman ilimi a jihar Oyo.
Asusun ba da lamunin karatu na Najeriya (NELFUND) ya sanar da ranar 24 ga Mayu, 2024, a matsayin ranar da za a bude shafin yanar gizo domin neman lamunin.
Dalibar da aka ci zarfi a makarantar Lead British International School, Namitra Bwala ta shigar da kara kotu tana neman a bita ta diyyar N500,000, 000.
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa tana shirin tallafawa masu hidimar kasa domin samar da matasa masu sana’akamar yadda Dr. Jamila Ibrahim ta bayyana.
Wani rikice ya barke a jami'ar Ibadan yayin da dalibai ke gudanar da zanga zanga kan karin kudin makaranta. Rundunar sojin da ke jamia'ar sun kama dalibai hudu.
Gwamnatin Kaduna karkashin jagorancin Malam Uba Sani ta bayyana shirinta na haɗe makarantu 359 da waɗanda ke wurare masu amince saboda matsalar ƴan bindiga.
Hukumar jami'ar ilimi, kimiyya da fasaha ta jihar Ekiti ta kori ɗalibai.mata biyu bisa laifin dukan da aka yi wa wata ɗaliba a wani faifan bidiyo da ya bazu a X.
Makarantar Islamiyya ta IOSSA a jihar Bauchi ta bayyana yadda ta horas da dalibanta yayin jarrabawar UTME inda da dama suka yi bajinta wurin samun maki mai kyau.
Wata daliba daga Arewacin Najeriya, Fatima Saleh Alkali ta burge mutanan kasar bayan samun maki 336 a jarrabawar UTME da aka gudanar a kwanakin baya.
Karatun Ilimi
Samu kari