Jihar Kano
Rahotanni sun bayyana cewa an harbi wani dan jarida da harsashi a gidan gwamnatin jihar Kano. Jami'an 'yan sanda sun fara gudanar da bincike kan lamarin.
Hukumar EFCC ta na zargin akalla tsofaffin gwamnoni 54 a Najeriya da badakalar N2.187trn yayin da suke mulkin jihohinsu daban-daban tun bayan dawowar dimukradiyya.
Wata babbar kotu a Kano ta hana jami'an tsaro da jam'iyyar APC amfani da jami'an wajen kama wadanda su ka kori tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje daga jam'iyyar.
Wata kotu a Kano ta dakatar da kamfanin KEDCO da hukumar NERC tilastawa kamfanoni biyan sabon kudin wutar lantarki har sai kotu ta kammala sauraron karar.
Hukumar tsaron farar hula ta NSCDC ta tabbatar da cafke masu safarar man fetur daga jihar zuwa Katsina.Ta kama litar mai dubu ashirin, kuma ta mayar da su gidan mai.
Rundunar 'yan sanda a Kano ta sanar da cafkewa tare da gurfanar da masu manyan laifuka 3000 cikin shekara guda. Kwamishinan yan sandan jihar ne ya bayyana hakan.
Wata dalibar aji uku a jami’ar kimiyya da fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil, Aisha Yahaya ta rigamu gidan gaskiya. An tsinci gawar wata dalibar a dakinta.
Kwamnadan Hisba na jihar Kano sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya ce sun sake sababbin tsare-tsare kan shirin auren zawarawa inda za a saka bangarori da dama.
Gwamnatin jihar Kano ta sanar da sanya dokar ta baci a harkar ilimi. Kwamishinan ilimi na jihar ne ya yi bayanin ranar Litinin da ta wuce a jihar Jigawa
Jihar Kano
Samu kari