Jihar Kano
Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta yi martani kan jita-jitar cewa NNPP ta yi zama don bar wa Abba Kabir kujerarshi da kuma koma wa jam'iyyar APC.
A wata hira, Eunice Atuejide ta bayyana cewa duk hukuncin da Kotun Koli za ta yanke sabanin abun da mutane ke so, wanda shine Abba zai haifar da tashin hankali.
Gabannin yanke hukunci, Sarakunan Hausawa a Kudu maso Yamma sun gargadi shugabannin siyasa da kada su cinnawa Najeriya wuta saboda zaben gwamnan jihar Kano.
Wani manazarci kan harkokin siyasa ya bayyaɓa cewa siyasar Kano zata yi tasiri a hukuncin da koli zata yanke wanda zai raba gardama tsakanin Abba Kabir da Gawuna.
Abdulmumin Jibrin ya hadu da shugaban kasa Bola Tinubu a Aso Rock a ranar Juma'a, sun tattauna a kan abin da ya shafi siyasar Kano da shugaban kasan.
Jigon jam'iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso ya ka ziyarar jaje a jihar Kaduna game da harin bam da sojoji su ka yi kan masu Maulidi a kauyen Tudun Biri.
Fitaccen mawakin suyasar nan, Dauda Adamu Abdullahi Kahutu Rarara tare da wasu jaruman Kannywood maza da mata sun roki mazauna Kano su rungumi zaman lafiya.
Hukumar yaki da cin hanci (EFCC) ta gurfanar da wani daraktan kamfani, Salisu Suleiman kan badakalar miliyan 21 na biyan kudaden iskar gas da bakin mai.
A cewar Zaura, canja kudin da Buhari ya yi ana dab da babban zaben kasar, ya jefa 'yan Najeriya cikin mawuyacin hali wanda ya tilasta su juya wa jam'iyyar baya.
Jihar Kano
Samu kari