Yan jihohi masu arzikin man fetur
Kungiyar Ijaw Youth Council (IYC) daga jihar Bayelsa ta bukaci Bola Tinubu ya sauya mukamin karamin Ministan man fetur, Heineken Lokpobiri saboda rashin kwarewa.
Shugaban kungiyar manyan ma'aikatan mai da iskar gas ta Najeriya, Festus Osifo, ya bayyana dalilan da suka sa ake ci gaba da ganin layin ababen a gidajen mai.
Masu ababen hawa da ke bin titin Anthony Oke zuwa Gbagada ta babbar hanyar Oshodi-Apapa sun tsallake rijiya da baya yayin da yanka dauke da gas ta fadi.
Kungiyar yan kasuwar man fetur (IPMAN) ta bayyanawa 'yan Najeriya cewa kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) ne ke jawo karancin fetur ta hanyar hana su mai.
Kwamitin majalisar wakilai na musamman kan satar danyen man fetur ya aika da gargadi kan barayin man fetur. Ya sha alwashin ganin bayan ayyukansu.
Rahotanni daga babban birnin tarayya Abuja da kuma wasu jihohin kasar nan sun nuna cewa farashin litar fetur ya kusa kaiwa N1000 yayin da wahalar mai ta tsananta.
Kamfanin mai na kasa (NNPCL) ya ce ya bankado tare da kwace mai daga wasu haramtattun matatun mai guda 63 da bututun satar mai 19 a yankin Neja Delta.
Hukumar hana yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) ta nemi gwamnatin tarayya ta samar da kotu na musamman saboda barayin fetur don saukaka hukunci.
Matatar man fetur ta Fatakwal da ke Ribas ta gaza fara aiki a watan nan duk da alkawarin da shugaban kamfanin NNPCL, Mele Kyari ya dauka na cewa za a fara aiki.
Yan jihohi masu arzikin man fetur
Samu kari