Gobara
Gobara ta ƙone tankar mai 2 da keke-nape 17 a gidajen man AA Ayagi da Al-Wahida a Kano ranar 14 ga Janairu, 2026; hukumar kashe gobara ta nemi a kiyaye tsaro.
Hukumar agajin gaggawa ta NEMA ta kai dauki wajen kashe gobara karamar hukumar Malumfashi a jihar Katsina. Fashewar wutar sola ne ya tayar da gobarar.
Shugabannin Musulunci a jihar Lagos sun nuna damuwa game da lalacewar babban masallaci mai tarihin shekaru 134 wanda gobara ta cinye da wasu gine-gine.
A labarin nanz, za a ji cewa kasuwar masu gyaran motoci ta gamu da mummunan iftila'i bayan gobara ta kama, ta ci ba ƙaƙkautawa na lokaci mai tsawo.
Gobara ta lalata ofisoshi da taskar makamai ta rundunar ‘yan sandan Mopol 13 a Makurdi, jihar Benue; rundunar ta tabbatar da faruwar lamarin tare da fara bincike.
Jami'an ceto suna kokarin kashe gobara a ginin Great Nigeria Insurance House da ke Lagos Island, inda mutane bakwai suka raunata yayin da aka ceto gine-gine da dama.
Wata mummunar gobara ta tashi a babbar kasuwar Jos da ke jihar Plateau. Gobarar ta lalata shagunan 'yan kasuwa da dama bayan ta tashi a cikin dare.
An samu asarar dukiya mai tarin yawa bayan da gobara ta lakume wata babbar kasuwa a birnin Kano. 'Yan kasuwar sun nemi gwamnati ta kawo musu dauki
Gobara ta lalata gidaje huɗu a Asokoro, Abuja, a wani gini da ake alakanta da tsohon gwamnan Zamfara, Ahmed Yerima. Ana zargin farantan solar ne suka jawo gobarar.
Gobara
Samu kari