Nade-naden gwamnati
Bayan yada jita-jitar korar Bello Matawalle, wata ƙungiya mai suna 'Guardians of One Nigeria' ta gargadi masu yaɗa labarin da ka da su dagula ayyukan ministan.
Hon. Mike Dio Jen ya yi murabus daga kujerar ɗan Majalisar dokokin jihar Taraba domin karɓar muƙamin kwamishina da Gwamna Agbu Kefas ya naɗa shi.
Fitaccen matashin dan siyasa, Musa Azare ya ki karɓar mukamin SSA da gwamnan Bauchi ya ba shi, yana mai cewa zai fi amfani idan ya ci gaba da aikinsa na shari’a.
Gwamnatin tarayya ta karyata rahoton da ke cewa an kori Ministoci uku, tana cewa labarin karya ne kuma barazana ga 'yancin fadar albarkacin baki.
Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed ya amince da nada sababbin masu taimaka masa na musamman a bangarori da dama guda 168 don karfafa shugabanci.
Kungiyar matasan APC daga Bauchi ta buƙaci a gudanar da bincike kan zargin cin zarafin ministan harkokin waje, Yusuf Tuggar da mataimakin gwamnan jihar ya yi.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi nade-nade masu yawa a gwamnatinsa tun bayan hawansa kan karagar mulki. Waau suna zarginsa da nuna bangaranci a rabon mukamai.
Kashim Shettima ya ja kunnen shugaban NAHCON, Farfesa Usman, da ya dakatar da gudanar da hukumar shi kaɗai tare da sanya kwamishinonin hukumar a harkokin gudanarwa.
Shugaban riko na jihar Rivers, Ibok-Ete Ibas, ya tabo batun gayyatar Gwamna Siminalayi Fubsra wanda aka dakatar domin fara bincikensa kan mukaman da ya nada.
Nade-naden gwamnati
Samu kari