Yan bindiga
Kungiyar Equipping The Persecuted ta yi gargadi kan yiwuwar hare-haren Kirsimeti a Arewa, DSS ta tabbatar da daukar matakan kariya yayin da ake shakku kan zargin.
Dan bindiga, Bello Turji ya fito da sabon bidiyo yana karyata zargin cewa Bello Matawalle ya ba ’yan bindiga kuɗaɗe, yana cewa ba a taba ba shi miliyoyi ba.
Shugaban karamar hukumar Bukkuyum a jihar Zamfara, Abubakar Umar Faru, ya yi tsokaci kan matsalar rashin tsaro. Ya ce sojoji na bukatar manyan makamai.
Ministan sadarwa ya bayyana dabarun da 'yan bindiga ke yi wajen yin amfani da waya ko yanar gizo. Ya ce suna amfani da wasu hanyoyi domin kaucewa kama su.
Kungiyar matan Arewa maso Yamma ta gargadi Bello Turji ya mika wuya kafin lokaci ya kure masa. Sun yaba wa sojojin Najeriya game da kashe mataimakin Bello Turji.
Fitaccen dan ta’adda, Bello Turji ya shiga tashin hankali bayan sojojin Najeriya sun kashe kwamandansa, Kallamu Buzu a kwanton-bauna da aka yi a Sabon Birni.
Rahotanni sun tabbatar da cewa mutane sun jikkata yayin da wani abin fashewa ya yi bindiga, ya tarwatse da matafiya a kan wani babban titi a jihar Zamfara.
’Yan bindiga sun kashe mataimakin shugaban karamar hukumar Bukuyum a Zamfara, Mu’azu Gwashi, duk da an biya su kudin fansa N15m bayan watanni shida.
Wani wanda ya bayyana kansa a matsayin tsohon hadimin karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle, ya ce ya shirya ba da shaida a gaban kotu a kansa.
Yan bindiga
Samu kari