Yan bindiga
Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya aika da sakon gargadi ga 'yan siyasa kan matsalar rashin tsaro. Gwamna Uba Sani ya bukaci su yi taka tsan-tsan.
Mutanen wasu kauyuka a jihar Kano na fuskantar matsalar hare-haren 'yan bindiga. Lamarin ya tilasta musu tserewa daga cikin gidajensu don neman mafaka.
Sheikh Ahmad Gumi ya ce ƴan bindiga ba sa kai hari babu dalili, yana mai kiran gwamnati da ta nemi sulhu da su domin samun zaman lafiya a Najeriya.
Majalisar Wakilai ta yi Allah-wadai da harin da ’yan bindiga suka kai wa konboyin dan majalisa Jafaru Mohammed Ali a Neja, inda jami’an tsaro suka mutu.
Gwamnatin Kaduna ta ce ta ceto mutane 500 daga hannun ‘yan bindiga ba tare da biyan kudin fansa ko amfani da karfin makami ba. Kwamishina ya yi bayani.
Jami'an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA), sun cafke wata mata dauke da alburusai da ake zargin za ta kai wa 'yan bindiga a Zamfara.
Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya yabawa dakarun sojojin Najeriya kan kisan da suka yi wa 'yan bindiga a jihar Kano.
Ƴan sanda a jihar Delta sun kama masu garkuwa uku, sun kwato N4.1m na kudin fansa da bindigar AK-47, sun kuma ceto wata mata da aka sace a Obinomba.
Rahotanni sun tabbatar da cewa wasu yan bindiga sun shiga kauyen Doguwar Dorawa a karamar hukumar Bakori, jihar Katsina, sun yi wa mutum 2 yankar rago.
Yan bindiga
Samu kari