Jihar Borno
Jami'an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA), ta sanar da samun nasarar cafke wani mai safarar miyagun ƙwayoyi ga 'yan ta'adda a jihar Borno.
'Yan ta'addan Boko Haram dauke da muggan makamai sun kai sabon harij ta'addanci a jihar Yobe. 'Yan ta'addan sun halaka mutum uku ciki har da wani jami'in dan sanda.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum ya shirya karya farashin man fetur ga manoma don inganta noma yayin da ake ci gaba shan fama a Najeriya.
Mayakan kungiyar 'yan ta'addan Boko Haram sun kai sabon hari a jihar Yobe. Miyagun 'yan ta'addan sun halaka mutum biyu tare da sace wasu mutum uku.
Tsohon gwamnan jihar Yobe, Bukar Abba Ibrahim, ya yi bankwana da duniya yana da shekara 73. Tsohon gwamnan ya rasu ne a kasar Saudiyya inda yake jinya.
Mayakan kungiyar ta'addanci sun kai mummunan hari ofishin 'yan sanda a yankin Nganzai dake jihar Borno. Sun bindige jami'an 'yan sanda hudu dake bakin aiki.
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi ta'aziyyar rasuwar Haja Hauwa, matar mahaifin mataimakin shugaban ƙasa wanda ta rasu ranar Alhamis a Maiduguri.
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya yi rashin matar mahaifinsa wacce ta rasu tana da shekara 69 a duniya. Ta rasu ne bayan ta yi jinya.
Wani bam da ƴan ta'addan Boko Haram suka dasa ya tashi da wasu mutane a jihar Borno. Bam ɗin dai ya yi sanadiyyar halaka mutum 12 yayin da wasu suka jikkata.
Jihar Borno
Samu kari