A Karshe, Kwankwaso Ya Yi Murabus daga NNPP, Ya Jero Manyan dalilan Barinta

A Karshe, Kwankwaso Ya Yi Murabus daga NNPP, Ya Jero Manyan dalilan Barinta

  • Tsohon gwamnan Knao, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya tabbatar da yin murabus daga daga jam’iyyar NNPP mai adawa
  • Kwankwaso ya bayyana wannan mataki da ya dauka a matsayin mai wahala, yana mai cewa sauyin siyasa a kasa ya tilasta masa haka
  • Rahotanni sun nuna cewa Kwankwaso na shirin komawa ADC inda ake sa ran zai bayyana matsayarsa a Kano nan ba da jimawa ba

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar NNPP mai adawa a Najeriya.

Jagoran siyasar Kwankwasiyya ya bayyana cewa yana bukatar sake daidaita tafiyar siyasarsa domin nasara a zaben 2027.

Kwankwaso ya yi murabus daga jam'iyyar NNPP
Dandazon yan Kwankwasiyya da jagoransu, Rabiu Kwankwaso a Kano. Hoto: Rabiu Musa Kwankwaso.
Source: Facebook

Legit Hausa ta samu wannan bayani ne daga shafin Sanatan wanda ya wallafa a Facebook a yau Lahadi 29 ga watan Maris, 2026.

Kara karanta wannan

2027: Hadimin Buhari ya rabu da APC, ya koma jam'iyyar hamayya a Kano

Musabbabin ficewar Kwankwaso daga NNPP

Kwankwaso, wanda ya tsaya takarar shugaban kasa a zaben 2023 a karkashin jam’iyyar, ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

A cikin rubutun da ya yi a Facebook, Kwankwaso ya ce:

“Ina sanar da ficewata daga jam’iyyar NNPP nan take."

Tsohon gwamnan ya bayyana cewa ya dauki wannan mataki ne bisa la’akari da yadda siyasar Najeriya ke tafiya a yanzu, wanda ke bukatar sabon tsari mai inganci.

Ya kara da cewa ya ga dacewar komawa wata dandalin siyasa da zai ba shi damar taimakawa wajen kawo sauyi a kasar yadda ya kamata.

Kwankwaso ya fadi dalilin barin NNPP
Sanata Rabiu Kwankwaso yana jawabi ga al'ummar Kano. Hoto: Rabiu Musa Kwankwaso.
Source: Facebook

Godiya da Kwankwaso ya yi ga NNPP

Kwankwaso ya gode wa shugabannin jam’iyyar, ciki har da shugabanta, Ajuji Ahmed, da sauran mambobi bisa goyon bayan da suka ba shi.

Haka kuma ya yabawa dukkanin shugabanni daga matakin kasa zuwa jiha da kuma gunduma, yana mai cewa sun taka muhimmiyar rawa a tafiyarsa.

Kara karanta wannan

Asiri ya tonu: An gano ɗan takarar shugaban ƙasa da PDP za ta marawa baya a 2027

Ya kuma yaba wa magoya bayan tafiyar Kwankwasiyya tare da sauran masu goyon bayan jam’iyyar bisa jajircewarsu da goyon bayansu.

Kwankwaso ya ce za su ci gaba da hada kai domin gina kyakkyawar makoma ga Najeriya domin inganta rayuwar talakawa a kasar.

Sai dai bai bayyana jam’iyyar da zai koma ba a hukumance, duk da cewa rahotanni sun nuna yana shirin shiga ADC.

Majiyoyi sun ce ana sa ran zai bayyana komawarsa sabuwar jam’iyya a Kano, inda manyan shugabannin jam’iyyar za su tarbe shi.

An kuma ruwaito cewa tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya karbi bakuncin Kwankwaso a Abuja, inda suka tattauna kan halin da kasar ke ciki.

An fara hasashen tikitin Kwankwaso, Obi

Tun farko, kun ji cewa maganar hadakar Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso na kara daukar hankali yayin da APC ke ci gaba da karfafa iko.

Wasu na ganin hadakar za ta kawo sauyi a zaben 2027, yayin da wasu ‘yan siyasa ke cewa ba za ta zama barazana ga gwamnati ba.

Rahotanni sun nuna cewa ana tattaunawa a boye kan tikitin hadaka, amma har yanzu akwai sabani kan wanda zai yi jagoranci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.