APC Tana cikin Matsala, Maganar Tikitin Kwankwaso da Obi Ya Fara Jan Hankali

APC Tana cikin Matsala, Maganar Tikitin Kwankwaso da Obi Ya Fara Jan Hankali

  • Maganar hadakar Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso na kara daukar hankali yayin da APC ke ci gaba da karfafa iko
  • Wasu na ganin hadakar za ta kawo sauyi a zaben 2027, yayin da wasu ‘yan siyasa ke cewa ba za ta zama barazana ga gwamnati ba
  • Rahotanni sun nuna cewa ana tattaunawa a boye kan tikitin hadaka, amma har yanzu akwai sabani kan wanda zai yi jagoranci

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Rahotanni sun nuna cewa yiwuwar hadakar siyasa tsakanin Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso na kara haifar da farin ciki a tsakanin wasu ‘yan Najeriya.

Hakan na zuwa ne bayan shirin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na komawa ADC a ranar Litinin 30 ga watan Maris, 2026.

An fara hasashen tikitin Kwankwaso da Obi
Sanata Rabiu Kwankwaso da Peter Obi. Hoto: Mr. Peter Obi, Rabiu Musa Kwankwaso.
Source: Twitter

Ana hasashen ADC za ta APC mamaki

Kara karanta wannan

Komai ya fito: Yadda Boko Haram ta saki bama bamai kan masu azumi a Borno

Rahoton Vangaurd na ganin wannan hadaka na iya zama kalubale ga APC mai mulki, wadda ke kara karfafa iko tun daga shekarar 2015.

A yanzu, APC na rike da mafi yawan jihohi da kujerun majalisa, lamarin da ke nuna yadda siyasa ke karkata zuwa bangare daya.

Rahoton ya ce wannan yanayi na iya rage gasa a siyasa tare da kara tasirin gwamnati a kan harkokin kasa baki daya.

A gefe guda, ana ci gaba da tattaunawa tsakanin bangarorin ADC kan yiwuwar hadakar Obi da Kwankwaso.

An ce akwai sabani a farko kan iko da tsarin jam’iyya da kuma wanda zai zama shugaban tikitin zaben 2027.

Sai dai ana ganin an samu sassauci a wasu bangarori, amma har yanzu batun wanda zai jagoranci tikitin na nan a bude.

Kwankwaso ya shirya fice wa daga NNPP zuwa ADC
Jagoran siyasar Kwankwasiyya, Rabiu Kwankwaso. Hoto: Rabiu Musa Kwankwaso.
Source: Twitter

Tasirin da tikitin Kwankwaso/Obi zai yi

A baya, kokarin hada kan ‘yan takarar biyu kafin zaben 2023 ya ci tura sakamakon rashin jituwa kan mukami.

Wasu masu sharhi na ganin hadakar za ta iya zama mai karfi idan aka hada karfin matasa na Obi da tsarin siyasar Kwankwaso.

Kara karanta wannan

Yakin Iran/Isra'ila ya fara sauya salo, jami'ai daga Rasha sun dura a Amurka

Sai dai wasu ‘yan siyasa sun rage tasirin hadakar, suna cewa ba za ta zama barazana ga shugaba Bola Ahmed Tinubu ba a zaben 2027.

Yadda Kwankwaso ke son ganin murmushin talaka

Kwankwaso dai ya sha fadin cewa babban abin da ya sanya a gaba shi ne ganin an samar wa talaka rayuwa mai inganci.

Ya sha sukar gwamnatin Bola Tinubu da APC kan yadda suka jefa yan Najeriya cikin mummunan hali inda ya ke shawartar yan kasar da su yi karatun ta natsu a zaben shekarar 2027.

Kwankwaso ya fara shirin kifar da Abba

Mun ba ku labarin cewa Sanata Rabiu Kwankwaso ya sake caccakar Gwamna Abba Yusuf kan butulce masa da ya yi bayan ya bar jam'iyyar NNPP ya koma APC gabanin 2027.

Kwankwaso ya bayyana cewa matakin sauya shekar gwamnan tamkar mutum ne ya dabawa kansa wuka, inda ya kira matakin da 'juyin kwakwalwa'.

Jagoran Kwankwasiyyar ya jaddada cewa Allah SWT ba zai bar wadanda suka ci amana ba, yayin da yake jaddada taken "falle daya ce" ga Abba a Kano.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.